An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
Published: 30th, March 2025 GMT
A birnin Roma masu goyon bayan al-ummar Falasdinu sun gudanar da zanga-zanga ta goyon bayan Falasdinawa, sun kuma ya allawadai da kungiyar tarayyar Turai da kuma Amurka kan yadda suka kasance manay-manyan masu taimakawa HKI a kissan kiyashin da take aikatawa a Gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa daubban wadanda suka fito kan tituna a tsakiyar birnin Roma na kasar Italiya suna rera taken ‘Free Free Palastine, wato yanci yanci Falasdinusun kammala ba tare da wata matsala ba.
Amma a jami’ar Colombia ta kasar Amurka rikicin rikicin jami’ar tare da masu goyon bayan kasar Falasdinu ya kaiga, shugabar jami’ar ta yi murabus daga matsayinta, don bada dama ga wani sabon shugaba, wanda zia aiwatar da shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na kawo karshen abinda ya kira ‘kin yahudawa a Jami’ar’.
Ya zuwa yanzu dai shugaban ya yanked alar Amurka miliyon 400 don takurawa shugabancin Jami’ar ta kawo karshen gangamin dalibai da kuma malaman jami’ar suke yin a goyon bayan Falasdinawa da samun yencin kasar.
Har’ila yau da goyon bayan yahudawan sahyoniyya a kissan kiyashin da take yi a kissan kiyashin da takewa al-ummar Falasdinu musamman a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: goyon bayan
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kasar Guinea Ta Yi Wa Musa Dadis Camara Afuwa
Shugaban gwamnatin soja na kasar Guinea Janar Mamadi Doumbouya ne ya yi wa tsohon shugaban sojan kasar Camara afuwa bayan da aka yanke masa zaman gidan kurkuku bisa laifin kisan kiyashin da ya faru a 2009 a birnin Conakry.
Kafafen watsa labarun kasar ta Guinea ne su ka sanar da afuwar da shugaba Mamadi ya yi wa Camara bisa dalilai na rashin lafiya.
Bugu da kari kakakin fadar shugaban kasa Janar Amara Camara wanda ya yi sanarwar ya ce, an yi hakan ne bisa shawarar da ma’aikatar shari’a ta gabatar.
Camara dai ya mulki kasar ta Guinea ne daga 2008-2009, an kuma yi masa shari’a ne a watan Yuli na 2024, saboda yadda a zamanin mulkin nashi aka yi amfani da karfi wajen murkushe ‘yan hamayya da su ka yi wani taro a cikin filin wasan kwallon kafa.
Fiye da mutane 150 ne dai su ka kwanta dama, kuma jami’an tsaron kasar su ka yi wa mata fiye da 100 fyade.
Shari’ar da aka yi wa Camara wacce ta sami cikakken goyon bayan MDD, ta same shi da lafin gajiyawa wajen hukunta masu laifi.
Matakin na gwamantin yanzu ya biyo bayan shirinta na biyan diyya ga iyalan wadanda aka kashe da kuma yi wa illa.
Sai dai kungiyoyin kare hakkin bil’adama a kasar suna sa alamun tambaya akan wannan matakin na yi wa adalci Karen tsaye.