Aminiya:
2025-04-01@09:42:12 GMT

Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone

Published: 30th, March 2025 GMT

Rahotanni sun ce, wani ɗan kasar China ya kama matarsa tana cin amanarsa da wanda ya ba ta aiki a lokutan aiki ta hanyar amfani da wata na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙi da ake sarrafa ta daga nesa, tana leƙen asiri daga nesa.

Mutumin mai hazaka da aka fi sani da Jing ya fara zargin cewa, matarsa na yin wata alaƙa ne bayan ta yi nisa sosai da shi kuma ta canza mu’amalarta sosai, ciki har da ziyartar iyayenta fiye da kowane lokaci da kuma kawo uzuri a duk lokacin da ya yi mata rakiya da kuma ƙarin lokaci a wurin aikinta.

Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah

Da yake kokawa kan batun, amma yana tsoron kada ya bayyana kansa ga matarsa idan har zarginsa bai tabbatar ba, Jing ya yanke shawarar yin amfani da na’urar ɗaukar hoto ta jirgi mara matuƙin na haya, don yi wa matarsa leƙen asiri daga nesa.

Yana tuƙa motarsa zuwa wurin aikinta sannan ya kunna jirgin mara matuƙi domin ya duba yankin ba tare da fargabar ganin matarsa ko abokan aikinta ba.

Wata rana yana lura da matarsa, sai ya hango ta fito daga ofishinta tare da wani mutum ta shiga mota da shi.

Sun yi tafiya zuwa wani wuri mai nisa a wajen wasu tsaunuka, inda jirgin mara matuki ya kama su suna rike da hannayensu, suna shiga cikin wani gida mara kyau.

Kusan mintuna 20 suna tare, daga nan sun bar gidan, sun koma wurin aikinsu.

Daga baya Jing ya shiga kafafen sada zumunta na zamani, inda ya bayar da rahoton cewa, mutumin da na’urar jirginsa mara matuki ya dauka a faifan bidiyo wanda da gaske ne ubangidan matarsa ne (wanda take yi wa aiki), kwanan nan ya yi mata karin girma.

“Mutumin da matar ke hulɗa dai shi, shi ne ya ɗauke ta aikin,” inda mijin ya rubuta a shafin sada zumunta na Weibo.

“Haka zalika yana aiki a masana’anta guda da matarsa, don haka bai yi musu dadi ba su ware wani wuri daban don yin alaka a can, saboda haka matata ta tilasta musu haduwa da shi a cikin daji.”

Jing ya kuma wallafa hotunan matarsa da masoyinta suna riƙe da hannayensu, ya kuma ce ya shirya yin amfani da bidiyon da na’urar ta ɗauka a matsayin shaida don neman raba aurensu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kwarto

এছাড়াও পড়ুন:

Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar

Rundunar sojin Amurka ta kaddamar da wani hari ta sama a ranar Asabar din da ta gabata kan mayakan IS a yankin Puntland na Somalia, inda suka kashe wasu mambobin kungiyar da dama, a cewar rundunar sojin Amurka .

A cikin wata sanarwa da ta fitar, rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Turai ta tabbatar da cewa, harin da aka kai tare da hadin gwiwar gwamnatin Somaliya, ya kashe da dama na mayakan ISIS a Somaliya.

Yayin da kungiyar IS ke hankoro hada karfinta a Somalia  wanda bai bunkasa ba idan aka kwatanta da kungiyar Al-Shabaab mai alaka da Al-Qaeda, kungiyar ta mayar da hankalinta ne wajen kara fadada karfinta a yankin Puntland mai cin gashin kansa.

“Harin ya auke ne a kudu maso gabashin Bosasso, Puntland, a arewa maso gabashin Somalia,” in ji sanarwar.

Wannan farmakin ya biyo bayan wani harin makamancin haka ne kwanaki biyu da suka gabata, wanda AFRICOM ta bayyana a matsayin wani babban shiri na yaki da ta’addanci a Somaliya.

A cikin watan Fabrairu, hare-haren da Amurka ta kai kan kungiyar IS a Puntland, hukumomin yankin sun  bayar da rahoton cewa an kashe “muhimman mutane”, ko da yake ba su bayar da karin bayani ba.

A wani mataki na kare martabar yankinta da kuma ja da baya kan rarrabuwar kawuna, rahotanni sun ce Somaliya ta bai wa Amurka damar  iko kan muhimman tashoshin jiragen ruwa da sansanonin jiragen sama dake Somaliland da Puntland.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne