‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
Published: 30th, March 2025 GMT
A jiya Asabar dubun dubatar ‘yan hamayyar siyasa su ka yi gangami a birnin Stanbul bayan da jam’iyyar “National Party” ta gayyace su, domin ci gaba da yin tir da kamun da aka yi wa Akram Imam Uglu wanda shi ne magajin garin na Stanbul.
Shugagan jam’iyyar “Turkish National Party’ ta adawa, Uzgur Ozil ya bayyana cewa adadin wadanda su ka halarci gangamin sun kai miliyan 2.
Daga cikin mahalarta gangamin da akwai mata da mahaifan Akram Ima wadanda su ka rika bayar da taken cewa za a ci gaba da yin gwgawarmaya ako’ina.”
Tun da asubahin jiya Asabar ne dai mutane su ka fara yin tururuwa a cikin birnin na birnin Sitanbul suna dauke da tutocin turkiya da kuma hotunan Mustafa Kamal Ataturk wanda ya kafa jamhuriyar Turkiya.
Tun bayan da aka kama Imam Uglu a ranar 19 ga watan Maris ne dai kasar ta Turkiya ta fada cikin dambaruwar siyasar wacce an dade ba a ga irinta ba.
Shugaban jam’iyyar hamayyar ya fadawa jaridar “ Lo Monde” ta Faransa cewa a kowace Asabar za su zabi garin da za su gudanar da Zanga-zanga,sannan kuma da kowane marecen Laraba a cikin birnin Sitanbul.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
Akwai karin tawagogin ceto da dama na kasar Sin da suka shiga ayyukan ba da agaji tare da takwarorinsu na Myanmar.
Girgizar kasar mai karfin maki 7.7 ta afku a kasar ce da ke kudu maso gabashin Asiya, a ranar Jumma’ar da ta gabata. A jiya Asabar da dare, tawagar yada labarai ta majalisar gudanarwar kasar ta bayyana cewa, sama da mutum 1,700 ne suka mutu, kana sama da 3,400 suka jikkata, yayin da kuma kimanin 300 suka bace, a kakkarfar girgizar kasar da ta faru a kasar ta Myanmar.
A yinin yau Lahadi kuma, wani jirgin saman kamfanin China Eastern Airlines ya tashi daga Kunming, babban birnin lardin Yunnan na kudu maso yammacin kasar Sin, dauke da kayayyakin agaji kimanin tan 7.3 zuwa kasar Myanmar da girgizar kasa ta afka wa.
An nemo kayayyakin agajin ne tare da tattara su a birnin na Yunnan, wadanda suka hada da tufafi, da magunguna, da taliya, da tantuna da sauran kayayyakin masarufi da ake bukata yau da kullum. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp