Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
Published: 30th, March 2025 GMT
Iyayen Abdulsalam Rabi’u Faskari, wanda aka sace tare da mahaifinsa a Jihar Katsina, sun bayyana cewa sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.
Abdulsalam, wanda ya lashe gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa da aka gudanar a Jihar Kebbi, an sace shi tare da mahaifinsa da wasu makonni biyu da suka gabata, bayan Gwamnan Katsina ya karrama shi.
Mahaifinsa, Malam Rabiu Zakariya Faskari, ya shaida cewa suna tsare a hannun ’yan bindiga a Katsina har sai da wani babban ɗan bindiga mai suna Yellow daga Zamfara ya zo ya karɓe su da ƙarfi.
“Ya yi wa masu garkuwa duka kafin ya tafi da mu,” in ji shi.
Ya ce an yi ciniki kan fansa amma Yellow ya ƙi yarda.
“Muna ta addu’a har ranar Juma’a da aka zo aka ce mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauke mu suka kai mu wani gari, daga nan muka yi tafiyar awa huɗu kafin muka samu mota.”
Malam Rabiu, ya ce da suka hau babur sai direban ya shaida musu cewa an kashe Yellow.
“Ashe mutuwarsa ce ta sa yaransa suka sake mu muka koma gida.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gasar Alƙur ani Gwarzo
এছাড়াও পড়ুন:
Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
Ta ce, sakamakon dukan da ta sha, ta samu karaya a kafa da kuma raunin da ya shafi kunnenta.
Sai dai Shu’aibu ya musanta wannan ikirarin, inda ya tabbatar da cewa, an kama dan uwanta ne a yayin wani samame da aka gudanar a wurin wani shagali a birnin Katsina.
A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne da laifin yin sojan gona da kuma yunkurin dakatar da jami’an Hisbah a lokacin da suke bakin aiki.
Da yake karin haske game da gaskiyar lamarin abinda ya faru, Shuaibu ya ce, an hana Hauwa shiga cikin ofishin Hisbah ne saboda irin tufafin da take sanye da su na rashin da’a, kuma ta yi yunkurin marin daya daga cikin jami’an Hisbah a lokacin da suka hana ta shiga.
Dangane da ikirarin da Hauwa ta yi na karaya a kafa, Shu’aibu ya ce hukumar ta bukaci iyalanta da su kawo mata shaidar na’urar haska kashi amma har zuwa lokacin taron manema labarai ba su samu wani takarda da ke tabbatar da raunin da ta samu ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp