Ba Za A Iya Dakile Ci Gaban Hakkin Dan Adam Na Xizang Da Kowace Irin Karya Ba
Published: 30th, March 2025 GMT
A bana aka cika shekaru 60 da kafuwar jihar Xizang mai cin gashin kanta ta kasar Sin. A ranar 28 ga watan Maris, wato ranar tunawa da ’yantar da miliyoyin bayi manoma a Xizang, gwamnatin kasar Sin ta fitar da wata takardar bayani mai taken “Ci gaban hakkin bil’adama a Xizang a sabon zamani”, wadda ta yi amfani da cikakkun bayanai na gaskiya don nuna yadda aka samu manyan sauye-sauye a jihar a cikin shekaru gommai da suka wuce.
“Ci gaba da aka samu a Xizang ya wuce yadda na yi zato, kuma mutane a nan suna rayuwa irin ta zamani sosai.” Wannan shi ne yadda babban dan jaridar kafar watsa labarai ta 24NewsHD ta kasar Pakistan Ali Abbas ya fada bayan ziyararsa a jihar. A cewarsa, karin mutane a duniya sun fahimci cewa, don neman kawo baraka ga kasar Sin ne wasu kasashen yammacin duniya suke kara wa miya gishiri a batun hakkin bil’adama a Xizang. Sannan game da batun ko an kiyaye hakkin bil’adama da kyau ko a’a a Xizang, bayanan sun riga sun ba da kyakkyawar amsa a kai, kana hakikanan labarun zaman rayuwar jama’ar jihar su ma sun bayyana gaskiya, don haka babu wata karya da za ta iya rufe ko kuma goge ainihin halin da ake ciki a jihar. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Abubuwan da suka sa Fafaroma Francis ya yi fice a duniya
Da safiyar wannan Litin fadar Vatican ta sanar cewa da misalin ƙarfe 7.35 Agogon Vatican Fafaroma Francis, wanda sunansa na asali Cardinal Jorge Mario Bergoglio, ya rasu a yayin da al’ummar Kirista na duniya ke bikin Ista.
Ya mutu ne washegari da ya fito bainar jama’a a Dandalin St Peter’s, domin taya Kiristoci murnar zagayowar ranar Ista.
Fafaroma Francis ya yi fama da doguwar jinya, inda a watan da ya gabata ne aka sallame daga asibiti bayan ya shafe makonni biyar can sakamakon cutar sanyin haƙarƙari mai tsanani.
Ga wasu abubuwa da Fafaroman ya yi fice a kansu:
1. Nuna adawa a fili ga wasu manufofin Donald Trump.Ya yi Allah wadai da yunƙurin Trump a mulkinsa na farko na gina katanga tsakanin Amurka da ƙasar Mexico, inda ya ce hakan ba ɗabi’ar Kiristoci ba ce.
Ya kuma yi Allah wadai da shirin maida baƙi ƙasashensu, da gwamnatin Trump ke ƙoƙarin yi a mulkinsa na biyu.
2. Sumbatar ƙafafuwan fursunoni.Fafaroma Francis ya wanke tafin ƙafafuwan wasu fursunonin gidan yarin Rome, tare da sunbata, abun da ya ja hankalin duniya.
3. Kira a magance matsalar sauyin yanayi.Fafaroma Francis ya zargi manyan ƙasashen duniya da ƙin ɗaukar matakan kare muhalli da sauyin yanayi, inda a 2023 ya ce wasu matsalolin ba za su taɓa gyaruwa ba.
4. Jawo masu ɗabi’ar auren jinsi a jiki.Duk da kakkausan suka da ya sha, wasu na ganin yana da ƙoƙarin jawo masu raunin imani a jiki, ciki kuwa har da yarda da ya yi ake sanya albarka ga auren jinsi.
5. Shi ne Fafaroma na 266, kuma na farko daga nahiyar Arewa da Kudancin Amurka.Asalin iyayensa ’yan Italiya ne, da suka yi ƙaura zuwa ƙasar Argentina. An haife shi a Buenos Aires, ranar 17 ga watan Disamba, 1936.
6. Kakkausar suka ga kamfanonin ƙera makamai.Ya yi kira ga ƙasashen duniya da su rungumi masalaha wajen magance rigingimu, gudun kada rikice-rikice su haifar da Yaƙin Duniya na 3.
7. Alaƙanta kwararar ’yan ci-rani zuwa Turai, da tauye ci-gaban ƙananan ƙasashe.Ziyararsa ta farko, Francis ya je tsibirin Lampedusa, yankin da ’yan ci-rani suke bi wajen shiga nahiyar Turai, inda ya ɗora laifi kan yadda ake tauye ci-gaban ƙananan ƙasashen duniya.
8. Yana son ƙwallon ƙafa da kuma waƙe-waƙe.Francis shi ne Fafaroma da yafi mu’amala da matasa, wajen sauraron su, da kuma ƙaunarsa da ƙwallon ƙafa.