Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
Published: 30th, March 2025 GMT
Jihar Lagos ta samu rahoton kamuwar matasa 10 da cutar Mashaƙo tsakanin ranar 1 ga Janairu zuwa 27 ga Maris 2025, yayin da hukumomin lafiya ke ƙara ƙoƙarin daƙile yaɗuwar cutar.
Kwamishinan lafiya na Jihar, Farfesa Akin Abayomi, ya bayyana cewa ana iya samun rahoton cutar har sama da 15 a rana. Daga cikin samfurorin da aka yi wa gwaji guda 76 an samu 10 da aka tabbatar da sun kamu, yayin da sauran samfurorin 63 sakamakonsu ya ke lafiya.
Abayomi ya bayyana cewa hukumomin lafiya suna gudanar da aikin tantancewa da bayar da magani cikin gaggawa, Gwamnatin jihar ta ci gaba da samar da tallafi, tare da samar da magani kyauta a asibitoci na gwamnati, inda aka tabbatar da samar da kayan da ake buƙata wajen tattara bayanai da haɗin kai tare da hukumar kiwon lafiya ta ƙasa da ta duniya.
Matakan da aka ɗauka suna tasiri wajen daƙile yaɗuwar ƙwayar cutar a cikin makon nan na baya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas
Kawo yanzu an samu aƙalla mutum biyar da suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar ruftawar wani bene mai bene mai hawa uku da ya ruguje a unguwar Ojodu-Berger da ke Jihar Legas.
Haɗarin ya faru ne da misalin ƙarfe 09.45 na safiyar ranar, inda hukumar kai ɗauki gaggawa tare da taimakon ’yan sanda suka gano cewa wani gini mai hawa uku ɗauke da gidan abinci da mashaya ne ya ruguje.
Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — ShettimaJami’in hukumar bayar da agajin, Ibrahim Farinloye, ya ce daga faruwar lamarin zuwa yanzu an ceto mutane 20 jimilla da suka maƙale a ƙarƙashin baraguzai.
“Sai dai abin takaicin shi ne cikin gawawwakin mamatan biyar da aka samu akwai mata uku da maza biyu.”
Shi ma da yake nasa jawabin a ranar Lahadi, babban Sakataren hukumar LASEMA, Olufemo Oke-Osanyintolu, ya ce mamatan biyar da aka samu an killace su a ɗakin ajiyar gawawwaki na asibiti.
Da farko dai babu labarin mutuwa, sai dai an samu asarar dukiya, amma yanzu bayan ci gaba da aikin ceto, an gano gawawwaki a cikin waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin baraguzai.
’Yan sanda da hukumar kai dauƙin gaggawa sun ci gaba da bincike domin gano musabbabin rugujewar ginin.
Jami’ai na hukumar LASEMA na ci gaba da binciken baraguzan ginin da nufin gano ko da sauran mutane a ciki.