Leadership News Hausa:
2025-04-22@07:57:42 GMT

Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina

Published: 30th, March 2025 GMT

Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina

A wani hatsarin mota da ya faru a hanyar Malumfashi-Kafur a Jihar Katsina, mutane tara sun rasu yayin da wasu 11 suka jikkata. Hatsarin dai ya shafi wata babbar motar bas da ke ɗauke da fasinjoji 20. 

Aliyu Ma’aji, Kwamandan Hukumar Kiyaye  Haɗɗura ta ƙasa (FRSC) a jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Ya bayyana cewa binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa gaggawar tuki ne ya haifar da hatsarin, inda direban ya rasa ikon sarrafa motar.

An Gabatar Da Motar Asibiti Ta Farko Mai ISO Na Matsayin Kasa Da Kasa A Hukumance Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Kano – FRSC

Haɗarin ya yi sanadin mutuwar mutane tara da ke cikin wata babbar motar bas mai ɗauke da fasinjoji 20, yayin da aka ceci wasu 11 kuma ana jinyar su a asibiti,” in ji Ma’aji. Ya kuma yi kira ga direbobi su guje wa tuƙin gaggawa, jigilar fasinjoji fiye da kima da kuma rashin kulawa yayin lokutan bukukuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Nijeriya NDLEA, ta yi nasarar kama hodar iblis wadda aka ɓoye a cikin littattafan addini da ake shirin kaiwa Saudiyya.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Hukumar NDLEA ɗin ta fitar a ranar Lahadi.

Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari? Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas

Hukumar ta bayyana cewa ta kama ɗauri 20 na hodar iblis ɗin wanda jimillar nauyinsu ya kai giram 500 a cikin littattafan addini.

NDLEA ta ce jami’anta sun gano hodar ne a yayin da suke gudanar da bincike a wani kamfanin da ke jigilar kayayyaki a Legas a ranar Talata 15 ga Afrilun 2025, yayin da yake shirin kai kayayyakin zuwa Saudiyya.

Baya ga haka, hukumar ta NDLEA ta yi ƙarin bayani game da wasu jerin nasarori da ta samu a makon da ya gabata a ƙoƙarin da take yi na daƙile fataucin miyagun ƙwayoyi.

A wani kamfanin na daban da ke jigilar kayayyaki, hukumar ta NDLEA ta ce ta kama kilo 2.8 na tabar wiwin Loud wadda aka shigar da ita ƙasar daga Amurka.

A Kano, jami’an NDLEA sun kama wani matashi ɗan shekara 22 da haihuwa da ke sayar wa ‘yan fashi da haramtattun kayayyaki a lokacin da suke sintiri a hanyar Bichi zuwa Kano.

An kama matashin ne a ranar Lahadi, 13 ga watan Afrilun, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Katsina ɗauke da kwalabe 277 na allurar pentazocine a ɗaure a cinyarsa da kuma cikin al’aurarsa.

Haka kuma, an kama wani da ake zargi mai suna Mohammed Abdulrahman Abdulaziz, mai shekaru 43, a ranar Lahadin da ta gabata a unguwar Rimin Kebe da ke Nasarawa a Kano tare da sunƙin wiwi nau’in skunk 68, wanda nauyinta ya kai kilo 30.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
  • Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Wanke Gonakin Shinkafa Sama Da Hekta 10,000 A Neja
  • Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan