HausaTv:
2025-04-21@19:45:19 GMT

Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar

Published: 30th, March 2025 GMT

Rundunar sojin Amurka ta kaddamar da wani hari ta sama a ranar Asabar din da ta gabata kan mayakan IS a yankin Puntland na Somalia, inda suka kashe wasu mambobin kungiyar da dama, a cewar rundunar sojin Amurka .

A cikin wata sanarwa da ta fitar, rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Turai ta tabbatar da cewa, harin da aka kai tare da hadin gwiwar gwamnatin Somaliya, ya kashe da dama na mayakan ISIS a Somaliya.

Yayin da kungiyar IS ke hankoro hada karfinta a Somalia  wanda bai bunkasa ba idan aka kwatanta da kungiyar Al-Shabaab mai alaka da Al-Qaeda, kungiyar ta mayar da hankalinta ne wajen kara fadada karfinta a yankin Puntland mai cin gashin kansa.

“Harin ya auke ne a kudu maso gabashin Bosasso, Puntland, a arewa maso gabashin Somalia,” in ji sanarwar.

Wannan farmakin ya biyo bayan wani harin makamancin haka ne kwanaki biyu da suka gabata, wanda AFRICOM ta bayyana a matsayin wani babban shiri na yaki da ta’addanci a Somaliya.

A cikin watan Fabrairu, hare-haren da Amurka ta kai kan kungiyar IS a Puntland, hukumomin yankin sun  bayar da rahoton cewa an kashe “muhimman mutane”, ko da yake ba su bayar da karin bayani ba.

A wani mataki na kare martabar yankinta da kuma ja da baya kan rarrabuwar kawuna, rahotanni sun ce Somaliya ta bai wa Amurka damar  iko kan muhimman tashoshin jiragen ruwa da sansanonin jiragen sama dake Somaliland da Puntland.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a wani samame da ta gudanar cikin gaggawa tare da tabbatar da ganin an dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Yazid Abubakar ya fitar, ya ce a ranar 16 ga Afrilu, 2025, da misalin karfe 1:45 na rana, tawagar hadin guiwa da ta kunshi jami’an ‘yan sanda da kuma jami’an kare hakkin jama’a (CPG) suna sintiri a kan babbar hanyar Anka-Gummi, inda suka gano wata mota samfurin Peugeot 206 da suka yi garkuwa da su a gefen hanya.

 

A cewar sanarwar, ba tare da bata lokaci ba, tawagar jami’an tsaro ta fara gudanar da wani bincike na hadin gwiwa, wanda ya kai ga ceto mutane shida da aka yi garkuwa da su, yayin da mutanen da aka ceto suka koma ga iyalansu.

 

Ta ce kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya yabawa ‘yan sandan bisa gaggauwa da daukar matakin da suka dauka.

 

Ya nanata kwazon rundunar tare da sauran jami’an tsaro na ganin an ceto duk wadanda aka sace tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.

 

CP Maikaba ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da gaggauta kai rahoton duk wani abin da ba su gane ba ga jami’an tsaro mafi kusa da su domin kawo dauki cikin gaggawa.

 

Sanarwar ta kuma jaddada cewa, rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta wargaza maboyar barayi da kuma dawo da zaman lafiya mai dorewa a jihar.

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Wani Harin Amurka kan Yemen ya kashe fararen hula akalla 12
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Mayakan Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Sun Sake Kunno Kai A Garuruwan Deir ez-Zor Da Hasaka Na Siriya
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen