Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba
Published: 30th, March 2025 GMT
Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa, Iran ba ta shiga tattaunawa da Amurka kai tsaye ba, yana mai mayar da martini kan wasikar da shugaban Amurka ya aike mata, amma kuma ya bayyana cewa hakan zai bude kofa ga tattaunawar kai tsaye.
Da yake magana a wani taron majalisar ministocin a ranar Lahadi, Pezeshkian ya tabbatar da cewa an isar da martanin Iran ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump ta hanyar Oman.
Ya jaddada cewa, yayin da Iran ta yi watsi da tattaunawar kai tsaye, ba ta taba rufe kofar yin shawarwarin kai tsaye ba matukar dai aka cimma wani abu da bai yi karo da manufofin Iran ba.
Ya kara da cewa, “Kamar yadda Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta taba toshe hanyoyin yin shawarwari kai tsaye a baya ba, amsar wasikar ta kara tababtar da hakan, tare da tabbatar da cewa sakamakon tattaunawar da za a yi wadda ba ta kai tsaye ba, it ace za ta fayace yiwuwar yin tattanawar ta kai tsaye ko akasin hakan.
Shugaban na Iran ya alakanta kalubalen da ake fuskanta a tsarin tattaunawar da rashin matsaya guda daga bangaren Amurka, yana mai jaddada cewa dole ne Amurka ta gyara kura-kuran da aka yi a baya tare da maido da aminci da gaskiya da kuma cika alkawali.
Pezeshkian ya yi nuni da cewa, “Wannan zai zama gwaji a kan n yadda Amurkawa za su iya tabbatar da ci gaban tattaunawar.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
Jihar Lagos ta samu rahoton kamuwar matasa 10 da cutar Mashaƙo tsakanin ranar 1 ga Janairu zuwa 27 ga Maris 2025, yayin da hukumomin lafiya ke ƙara ƙoƙarin daƙile yaɗuwar cutar.
Kwamishinan lafiya na Jihar, Farfesa Akin Abayomi, ya bayyana cewa ana iya samun rahoton cutar har sama da 15 a rana. Daga cikin samfurorin da aka yi wa gwaji guda 76 an samu 10 da aka tabbatar da sun kamu, yayin da sauran samfurorin 63 sakamakonsu ya ke lafiya. Kwamishinan ya ƙara da cewa cutar ta afkawa ƙananan hukumomi da dama, inda Eti-Osa ta fi yawan wanda abin ya shafa.
Kisan Mummuken Cutar Mashako A Nijeriya Da Sassan Duniya Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) IIAbayomi ya bayyana cewa hukumomin lafiya suna gudanar da aikin tantancewa da bayar da magani cikin gaggawa, Gwamnatin jihar ta ci gaba da samar da tallafi, tare da samar da magani kyauta a asibitoci na gwamnati, inda aka tabbatar da samar da kayan da ake buƙata wajen tattara bayanai da haɗin kai tare da hukumar kiwon lafiya ta ƙasa da ta duniya.
Matakan da aka ɗauka suna tasiri wajen daƙile yaɗuwar ƙwayar cutar a cikin makon nan na baya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp