Hukumar Ƴansandan Jihar Kano ta kama wani matashi mai shekaru 20, Usman Sagiru, bisa zargin kashe wani ɗan Bijilanti a tawagar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II bayan Sallar Eid. Iftila’in ya faru ne da ƙarfe 12:40 na rana a Lahadi, lokacin da ayarin Sarkin Kano ke watsewa daga filin Sallar Idin.

A cewar kakakin Ƴansanda SP Haruna Kiyawa, ana zargi Sagiru da wasu da suka tsere da soka makami ga wani ɗan sa kai mai suna Surajo Rabiu daga unguwar Sabon Titi Jaba, wanda ya mutu sakamakon raunin.

Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II

Wani ɗan Bijilanti, Aminu Suleman daga Kofar Mata, shi ma ya jikkata a harin wanda yana yanzu yake jinya a Asibitin Murtala Muhammad na Jihar Kano. Waɗannan ‘yan sa kai sun kasance cikin tawagar da ke kare Sarkin Kano a lokacin harin. ‘Yansandan sun bayyana cewa sun fara cikakken bincike kan lamarin, inda suka kuma gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin yi masa tambayoyi dangane da lamarin.

Hukumar ta sake nanata haramcin duk wani irin hawan Sallah a jihar, tare da gargadin cewa za a kai duk wanda aka tarar yana shiga irin waɗannan ayyuka gaban doka. A cewar sanarwar, ‘yan sandan sun dage kan yaƙi da daba da duk wani aiki da zai haifar da tarzoma a jihar, musamman ma a yayin da ake shirye-shiryen bikin Sallah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi

Ana tuhumar wata ma’aikaciyar kamfanin masaka a Jihar Goias ta ƙasar Brazil da laifin saka wa abokan aikinta guba bayan ta yi jayayya da su a kan abin da matar ta kira da rashin adalci wajen ƙarin matsayi da kamfanin ya yi.

Lamarin ya faru ne a wata masana’anta da ke Abadia de Goias, wani gari a yankin Goiânia Metropolitan.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari

’Yan sanda sun yi iƙirarin cewa, kyamarar daukar hoto cikin sirri (CCTV) ta kama wadda ake zargin mai shekara 38 tana buɗe wasu gorunan abin sha, wanda daga bisani wata ma’aikaciya ta sha, inda ta ji wani zafi a makogwaronta.

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa, an sami wani nau’in ɗanɗano mai ƙarfi a cikin ruwan, wanda ke nuna cewa, wacce ake zargi da laifin tana son zuba wa abokan aikinta guba.

Shaidu sun bayyana cewa, matan biyu abokan juna ne, amma dangantakarsu ta yi tsami bayan ɗaya daga ciki ta samu ƙarin girma, wanda bai yi wa wadda ake zargi da laifin daɗi ba.

Sun yi ta jayayya, wanda ake zargin lamarin ya kai ga matakin zuba gubar.

’Yan sandan yankin sun shaida wa manema labarai cewa, wanda ake zargin mai shekara 38, ta kuma shiga ɓangaren da ake ajiye sinadarai na kamfanin, ba tare da izini ba.

An yi imanin cewa, ta haka ne aka gano ta yi amfanin da sinadaran a matsayin guba.

Bayan ɗaya daga cikin ma’aikatan ta sha, ta gano cewa akwai matsala, inda ta kira motar ɗaukar marasa lafiya, aka garzaya da ita asibiti domin duba ta, amma ta warke sarai, sai dai likitoci sun ce, an yi yunƙurin kashe ta.

‘Yan sanda sun kama wadda ake zargin a ranar 27 ga Fabrairu, bayan sun duba kyamarori na CCTV don gano abin da ake zargin ta, kuma ta amince da gurbata abin shan ga abokan aikinta bayan sun yi wata jayayya.

Mai yiwuwa za a tuhume ta da laifin yunƙurin kisan kai, wanda ke da hukuncin ɗaurin shekar 6 zuwa 20 a gidan yari.

Yadda kyamara ta ɗauki hoton matar tana aika-aikar

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Gwamna Abba ziyarar barka da Sallah
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone