Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
Published: 31st, March 2025 GMT
Hukumar Ƴansandan Jihar Kano ta kama wani matashi mai shekaru 20, Usman Sagiru, bisa zargin kashe wani ɗan Bijilanti a tawagar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II bayan Sallar Eid. Iftila’in ya faru ne da ƙarfe 12:40 na rana a Lahadi, lokacin da ayarin Sarkin Kano ke watsewa daga filin Sallar Idin.
A cewar kakakin Ƴansanda SP Haruna Kiyawa, ana zargi Sagiru da wasu da suka tsere da soka makami ga wani ɗan sa kai mai suna Surajo Rabiu daga unguwar Sabon Titi Jaba, wanda ya mutu sakamakon raunin.
Wani ɗan Bijilanti, Aminu Suleman daga Kofar Mata, shi ma ya jikkata a harin wanda yana yanzu yake jinya a Asibitin Murtala Muhammad na Jihar Kano. Waɗannan ‘yan sa kai sun kasance cikin tawagar da ke kare Sarkin Kano a lokacin harin. ‘Yansandan sun bayyana cewa sun fara cikakken bincike kan lamarin, inda suka kuma gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin yi masa tambayoyi dangane da lamarin.
Hukumar ta sake nanata haramcin duk wani irin hawan Sallah a jihar, tare da gargadin cewa za a kai duk wanda aka tarar yana shiga irin waɗannan ayyuka gaban doka. A cewar sanarwar, ‘yan sandan sun dage kan yaƙi da daba da duk wani aiki da zai haifar da tarzoma a jihar, musamman ma a yayin da ake shirye-shiryen bikin Sallah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tawagar CPPCC Ta Ziyarci Nijeriya Da Cote d’Ivoire Da Senegal
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp