Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
Published: 31st, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya taya al’ummar Musulmi murna bisa kammala azumin watan Ramadan lafiya, tare da kira garesu da su rungumi koyarwar Annabi Muhammadu (S.A.W) a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.
Ya bayyana hakan ne a sakon sa na Sallah ga al’ummar jihar.
Malam Umar Namadi ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da ya karɓi azumi da addu’o’in al’ummar Musulmi da suka yi a watan na Ramadan.
Haka kuma, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya ci gaba da yi wa shugabanni jagorancin don yin abin da ya dace domin jin daɗin al’umma.
Namadi ya kuma yi addu’ar samun zaman lafiya, da hadin kai, da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.
Radiyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamnan ya kuma karɓi manyan baki da suka kai masa gaisuwar Sallah a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista
Shugaba Vladimir Putin a yau Asabar ya umarci sojojin Rasha da su tsagaita buɗe wuta a Ukraine a wanan ranar ta Ista da kuma gobe Lahadi.
Putin ya kuma yi kira ga Kyiv da ta yi hakan, yayin da ake ganin tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura.
Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?Haka kuma, Rasha da Ukraine sun yi musayar fursunonin yaƙi na sama da mutum 500 — kuma mafi girma tun bayan fara yaƙi a tsakanin kasashen biyu.
Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelenskiy, ya ce ƙasarsa ta karɓi sojoji fursunonin yaƙi akalla 277 waɗanda ke tsare a gidajen yarin Rasha, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Telegram.
Ita ma ma’aikatar tsaron Rasha ta ce ta karɓi sojojinta 246 daga Kiev, waɗanda a halin yanzu ke ƙasar Belarus wacce ke kawance da Rasha kafin daga bisani a maida su gida.
Kazalika, hukumomin Moscow da Kiev sun jinjina wa UAE wajen gudanar da wannan gagarumin aiki cikin kwanciyar hankali.
Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa dai ce ta shiga tsakani wajen ganin an yi musayar fursunonin cikin nasara tsakanin ƙasashen biyu da suka shafe shekaru uku suna gwabza yaƙi.
Bayanai sun ce Rasha ta kuma yi iƙirarin cewa ta kusan ƙwato yankunan da sojojin Ukraine suka mamaye tun lokacin bazarar shekara ta 2024 a yankin Kursk da ke kan iyakar Rasha.
Ƙasashen duniya na ci gaba da kira na ganin an kawo ƙarshen wannan yaƙi, duk da cewa Rashan da Ukraine kowanensu na iƙirarin samun galaba a yaƙin.