Aminiya:
2025-04-01@21:13:27 GMT

Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda

Published: 31st, March 2025 GMT

Wani yaro dan shekara hudu da ya kira wayar salular ’yan sandan yankin Mount Pleasant a Karamar Hukumar Charleston Jihar South Carolina da ke Amurka ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a hukunta ta, a kai ta gidan yari saboda aikata hakan.

A cewar ’yan sanda yaron dan shekara 4 ya yi kururuwa, inda ya kira ’yan sanda bayan mahaifiyarsa ta shanye masa ice cream dinsa.

Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano

Al’amarin ya faru ne a cikin a garin Mount Pleasant, Wisconsin — mai nisan kilomita bakwai, yamma da Racine — lokacin da yaro dan shekara 4 ya tuntubi ‘yan sanda, inda ya ce, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa ba, a cewar wata sanarwa da ’yan sandan kauyen Mount Pleasant suka fitar.

“An aika jami’an ’yan sanda, wato Gardinier da Ostergaard don amsa kiran mai korafin neman agajin jami’an 911, wanda ya bayyana cewa, mahaifiyarsa ba ta kyauta masa kuma yana bukatar a kai ta gidan yari”, in ji hukumomi.

Lokacin da jami’ai suka isa gidansu, yaron ya ce, mahaifiyarsa ta shanye masa ‘ice cream’ dinsa kuma yana bukatar a ka ita gidan yari saboda aikata hakan.

Daga bisani ya kuma shaida wa ’yan sanda cewa, ba ya son a kai mahaifiyarsa gidan yari kawai, yana son a biya shi ‘icecream’ da ta shanye masa.

Daga baya jami’an sun bar gidan bayan sun gano cewa, wannan shi ne dalilin da ya sa aka kira su, amma sun dawo washegari, wanda a wannan karon suka ba wa yaron mamaki, inda suka kawo masa ice cream, “bayan ya yanke shawarar cewa ba ya son mahaifiyarsa ta shiga matsala,” in ji ’yan sanda.

Jami’an ’yan sandan da suka amsa kiran, ba su kaɗai ne suka gano abin dariya game da lamarin ba.

“Ban ce yana da gaskiya ba. Abin da nake fada shi ne na fahimta,” in ji wani mutum da ke mayar da martani ga ofishin ’yan sanda na kauyen Mount Pleasant game da lamarin a shafukan sada zumunta na zamani.

“Aƙalla ya san yadda ake kiran lambar taimako ko neman agajin jami’an tsaro,” in ji wata. “Zai iya ceton ran wani wata rana!”

Jami’an ’yan sandan da suka ziyarci gidan su yaron sun dauki hoto tare da yaron mai shekara 4 bayan an warware matsalar, inda suka samu damar yin barkwanci.

“Ina son jin labarin jami’anmu game da abin ban mamaki, inda suke samar da kyakkyawar dangantaka tsakaninsu da yara,” in ji wani mai amfani da kafofin sada zumunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yaro mahaifiyarsa ta

এছাড়াও পড়ুন:

DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.

Babban Darakta Muryar Najeriya VON, Malam Jibrin Baba Ndace ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su kara kaimi wajen addu’o’in samun nasara ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa tsarinta na sabunta fata.

 

Ya yi wannan kiran ne a cikin sakonsa na Sallah ga al’ummar Musulmi da aka rabawa manema labarai a Minna jihar Neja.

 

Malam Jibrin Baba Ndace ya tunatar da ’yan Najeriya cewa ya zama wajibi saboda nasarar da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta samu ya kasance nasarar mu baki daya, don haka akwai bukatar mu kasance cikin nasara.

 

Daga nan sai ya mika gaisuwar ban girma ga daukacin al’ummar Musulmin Nijeriya da ma na duniya baki daya na bikin sallah karama tare da shawartar su da su dage wajen tallafa wa aikin Nijeriya domin samun sakamako mai ma’ana.

 

A cewarsa a madadin daukacin mahukunta da ma’aikatan gidan rediyon Muryar Najeriya, ina mika sakon gaisuwa da jinjina ga daukacin al’ummar musulmin Nijeriya da ma na duniya baki daya a daidai lokacin da muke gudanar da bukukuwan karamar Sallah mai albarka tare da shawartar su da su aiwatar da abin da suka koya a cikin azumin watan Ramadan.

 

Malam Jibrin Baba Ndace ya yi addu’ar Allah ya karawa ‘yan Najeriya farin ciki da walwala, da kuma sabon karfi domin su ci gaba da hada kai wajen samar da fahimtar juna, wajen bayar da gudunmawa mai kyau ga ci gaba da zaman lafiyar Nijeriya.

 

PR ALIYU LAWAL

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano
  • Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda
  • Nigeria: Zazzabin “Lassa” Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 118 Tun Farkon Wannan Shekara
  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu