Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa gwamnatin JMI ta yi watsi da tattaunawa kai tsaye dangane da shirinta na makamashin Nukliya, sannan ya kara da cewa amma tattaunawa tare da masu shiga tsakani a bude take.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban yana cewa tuni, mun bawa gwamnatin Amurka amsar wasikar da ta aiko mana, inda a cikinta, muka kara jaddada cewa babu wata tattaunawa kai tsaye da Amurka, kuma an tura wasikar ta inda na Amurkan ta fito wato ta kasar Omman.

Don haka muna jiran matakan da Amurka zata dauka a kan amsar.

Daga karshe shugaban ya kammala da cewa duk wata mu’amala da gwamnatin kasar Amurka ba zai taba yiyuwa kai tsaye ba, wannan kuma saboda mummunan tarihin da Amurkawa suke da shin a karya al-kawali a duk wata yarjeniyar da aka cimma da ita a baya.

Ya dukkan tarihin JMI bata taba sabawa alkawalin da ta dauka da wata kasa ba, amma gwamnatin Amurka kuma tana da mummunan tarihi na sabawa alkawali don haka a halin yanzu ya rage mata ta sauya halayenta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta gayyaci mai kula da harkokin kasar Switzerland da ke Tehran domin nuna fishi kan irin munanan ayyukan Isra’ila a yankin da kuma barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Babban daraktan ma’aikatar harkokin wajen Iran Issa Kameli ne ya gayyaci jami’in diflomasiyyar na Switzerland, wanda kasarsa ke wakiltar muradun Washington a Tehran, yau Litinin.

Kameli ya mika gargadin na Iran a hukumance ga wakilin kasar Switzerland dangane da duk wani aiki na barna tare da bayyana aniyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran na mayar da kakkausan martani cikin tsauri kan duk wata barazana.

Jami’in diflomasiyyar na Iran yayi tir da kalaman tunzura tashe-tashen hankula wandanda kuma suka sabawa dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.

Wakilin na Switzerland ya ba da tabbacin cewa nan take zai isar da sakon Iran ga gwamnatin Amurka.

A ranar Asabar ne Trump ya ce za a kai wa Iran hari idan ba ta kulla yarjejeniya da Amurka ba.

“Idan ba su kulla yarjejeniya ba, za a ji bama-bamai,” in ji shi a wata hira da NBC News. Ya kuma yi barazanar ladabtar da Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne