An Fara Yakin Neman Zabe A Kasar Gabon
Published: 31st, March 2025 GMT
Jam’iyyun siyasa a kasar Gabon sun fara yakin neman zabe wanda za’a gudanar a ranar 12 ga watan Afrilu na wannan shekara ta 2025 a jiya Asabar.
Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto shugaban kasar Riko Brice Clotaire Oligui Nguema wanda ya jagoranci juyin mulki wa tsohon shugaban kasar Ali Bongo, sannan daga baya ya sauka don ya sake dawowa da hanyar zabensa ya fara yakin neman zabe a jiya, inda yake kira ga mutanen kasar su zabe shi saboda kyautatuwar kasar Gabon.
A cikin watan Augustan shekara ta 2023 ne sojoji suka kifar da gwamnatin Ali Bongo wanda ya gaji babansa Umar Bongo bayan rasuwarsa ba tare da zabe ba.
A halin yanzu dai yan takara 8 ne suke neman wannan kujerar a zaben ranar 12 ga watan Afrilu. Idan ba’a sami wanda ya lashe zaben ba za’a sake gudanar da zabe tsakanin wadanda suka zo na daya da kuma na biyu a zagayen farko.
Shugaban kasa a Gaban, yana yin shugabnci na tsawon shekaru 7 a zagaye na farko idan ya sake tsayawa ya kuma ci zabe yayi zagaye na 2 wanda zai kaishi ga shekari 14 na shugabaci. Daga nan shi ba zai tsaya ba, kuma wani daga cikin danginsa ba zai tsaya ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
Da safiyar Yau Talata jiragen yakin HKI sun kai hare-hare akan unguwar Dhahiya dake Beirut tare da bayyana cewa ta kai wa wani kusa ne a kungiyar Hizbullah hari.
Harin na yau shi ne irinsa na biyu da HKI ya kai a unguwar Dhahiya tun daga tsagaita wutar yaki a cikin watan Nuwamba na shekarar da ta gabata.
Jiragen yakin na HKI sun yi shawagi a kasa-kasan birnin Beirut kafin aji karar fashewar abubuwa masu karfi.
Kafafen watsa labarai sun ambaci cewa jiragen sun kai harin ne akan wani dogon gini a cikin unguwar.
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa ya zuwa yanzu mutane 3 ne su ka yi shahada,yayin da wasu 4 su ka jikkata.
Masu ayyukan ceto sun nufi wurin da aka hai harin, domin daukar wadanda su ka jikkata zuwa abitocin da suke kusa.
Jotunan farko sun nuna yadda gine-ginen da suke yankin su ka illata, biyu daga cikinsu sun rushe baki daya.
Mazauna yankin sun ce, an kai harin ne a lokacin da mutane suke bacci, lamarin da ya haifar da firgici a tsakaninsu.
A ranar Asabar din da ta gabata dai babban magatakardar kungiyar Hizbulllah Sheikh Na’im Kassim ya yi gargadin cewa, Idan HKI ta ci gaba da keta yarjeniyar tsagaita wuta, sannan kuma ba a taka mata birki ba, to suna da zabin abinda za su yi.