Aminiya:
2025-04-02@00:53:35 GMT

Dalilin da muka soke Hawan Bariki — Masarautar Zazzau

Published: 31st, March 2025 GMT

Masarautar Zazzau ta sanar da soke Hawa Bariki a wannan sallar ta bana — daya daga cikin haye-hayen shagulgulan Sallah na al’ada da masarautar ke gudanarwa a washegarin idin karamar Sallah.

A bisa al’adar Hawan Bariki, Sarkin Zazzau ya kan kai wa Gwamna gaisuwar sallah tare da duk hakimansa yayin da mazauna za su yi dakon wadanda ke haye-hayen dawakan a gefen titi su ma suna yi wa Sarki gaisuwar ban girma.

Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana

Sarki yakan jagoranci tawagar masarautar ta Zazzau inda zai ratsa ta cikin garin Zazzau sannan ya shiga unguwar Sabon Gari inda zai ziyarci Gwamna a gidan da aka tanada tun zamanin turawan mulkin mallaka.

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun Masarautar Zazzau, Abdullahi Aliyu Kwarbai ya fitar, ya ce an soke hawan sakamakon dalilai na aikin gyaran titi da shimfida sabuwar kwalta da ake yi a kan hanyar Kofar Doka zuwa kwanar Agoro.

Ya ce wannan aikin hanya da ake kan yi zai kawo cikas ga masu haye-hayen dawakai da kuma al’umma baki daya.

“Saboda haka wannan shi ne dalilin da Masarautar Zazzau ta soke Hawan Barikin da ake gudanar a washegarin Sallah karama” a cewar sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Bariki masarautar zazzau Masarautar Zazzau

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya kai ziyara ga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, domin nuna alhini kan kisan gilla da aka yi wa matafiya dyan Arewa a Uromi. Harin da aka kai a ranar Alhamis ya haifar da mutuwar mafarauta da ke kan hanyar zuwa bikin Sallah. Gwamnan ya bayyana cewa an kama mutane 14 da ake zargi da hannu a kisan, kuma za a kai su Abuja domin ci gaba da bincike.

A yayin ziyarar, Gwamnan Okpebholo ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta taimaka wa iyalan wadanda aka kashe, yana mai nuni da cewa Shugaban kasa da Yansanda sun dauki matakai kan lamarin. “Za mu tabbatar an gurfanar da wadanda suka aikata wannan mugun aiki a gaban doka,” in ji Gwamnan. Sanata Barau ya amsa da yabon matakan gwamnatin Edo, yana mai cewa: “Dole ne a ci gaba da yin Adalci domin hana irin wannan bala’i a nan gaba.”

Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi

‘Yansandan sun kara da cewa za su ci gaba da yaki da duk wani yunkurin tayar da tarzoma a jihar. Gwamnan Edo ya kuma yi kira ga al’umma da su yi haƙuri, yana mai jaddada cewa jihar ba ta yarda da ‘yan daba ko dakar doka a hannu ba. “Edo ta kasance gida ne na zaman lafiya ga dukkan al’ummar Nijeriya, kuma za mu kiyaye wannan tarihi,” in ji Gwamnan

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah
  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Gwamna Abba ziyarar barka da Sallah
  • Nigeria: Zazzabin “Lassa” Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 118 Tun Farkon Wannan Shekara
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah