Aminiya:
2025-04-22@07:34:38 GMT

Dalilin da muka soke Hawan Bariki — Masarautar Zazzau

Published: 31st, March 2025 GMT

Masarautar Zazzau ta sanar da soke Hawa Bariki a wannan sallar ta bana — daya daga cikin haye-hayen shagulgulan Sallah na al’ada da masarautar ke gudanarwa a washegarin idin karamar Sallah.

A bisa al’adar Hawan Bariki, Sarkin Zazzau ya kan kai wa Gwamna gaisuwar sallah tare da duk hakimansa yayin da mazauna za su yi dakon wadanda ke haye-hayen dawakan a gefen titi su ma suna yi wa Sarki gaisuwar ban girma.

Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana

Sarki yakan jagoranci tawagar masarautar ta Zazzau inda zai ratsa ta cikin garin Zazzau sannan ya shiga unguwar Sabon Gari inda zai ziyarci Gwamna a gidan da aka tanada tun zamanin turawan mulkin mallaka.

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun Masarautar Zazzau, Abdullahi Aliyu Kwarbai ya fitar, ya ce an soke hawan sakamakon dalilai na aikin gyaran titi da shimfida sabuwar kwalta da ake yi a kan hanyar Kofar Doka zuwa kwanar Agoro.

Ya ce wannan aikin hanya da ake kan yi zai kawo cikas ga masu haye-hayen dawakai da kuma al’umma baki daya.

“Saboda haka wannan shi ne dalilin da Masarautar Zazzau ta soke Hawan Barikin da ake gudanar a washegarin Sallah karama” a cewar sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Bariki masarautar zazzau Masarautar Zazzau

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar

“Mun zo nan ne a madadin gwamnatin tarayya domin ganowa da kuma jajanta muku rashin da aka yi, muna so mu tabbatar muku da cewa jami’an tsaro za su kawo karshen wannan kashe-kashen na rashin hankali.

 

“An yi mini cikakken bayani, kuma ina so in tabbatar muku cewa mun fahimci tushen wannan batu. Zamu kama wadanda suka aikata wannan aika-aika.

 

“Shugaban kasa ya damu matuka, kuma ya umarce mu da mu nemo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin su fuskanci shari’a, muna aiki tare da gwamnatin jihar domin daukar tsarin da zai hana faruwar wannan mummunan lamari, lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan hauka,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe
  • Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
  • NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi