Gwamnati Za Ta Inganta Wuraren Tarihi Domin Nishadantarwa A Duk Jihohin Nijeriya
Published: 31st, March 2025 GMT
Jagunlabi ya ce za a gudanar da shirin ne tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi domin mayar da wuraren tarihi zuwa wuraren shakatawa domin samar da kudin shiga wanda hakan zai haifar bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi a fannin fasaha da nishadi.
Ya bayyana cewa, aikin zai mayar da hankali ne wajen maidowa tare da kiyaye wuraren tarihi, kayayakin tarihi, da inganta ilimin al’adu da inganta sana’o’in cikin gida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
Babban Darakta Muryar Najeriya VON, Malam Jibrin Baba Ndace ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su kara kaimi wajen addu’o’in samun nasara ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa tsarinta na sabunta fata.
Ya yi wannan kiran ne a cikin sakonsa na Sallah ga al’ummar Musulmi da aka rabawa manema labarai a Minna jihar Neja.
Malam Jibrin Baba Ndace ya tunatar da ’yan Najeriya cewa ya zama wajibi saboda nasarar da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta samu ya kasance nasarar mu baki daya, don haka akwai bukatar mu kasance cikin nasara.
Daga nan sai ya mika gaisuwar ban girma ga daukacin al’ummar Musulmin Nijeriya da ma na duniya baki daya na bikin sallah karama tare da shawartar su da su dage wajen tallafa wa aikin Nijeriya domin samun sakamako mai ma’ana.
A cewarsa a madadin daukacin mahukunta da ma’aikatan gidan rediyon Muryar Najeriya, ina mika sakon gaisuwa da jinjina ga daukacin al’ummar musulmin Nijeriya da ma na duniya baki daya a daidai lokacin da muke gudanar da bukukuwan karamar Sallah mai albarka tare da shawartar su da su aiwatar da abin da suka koya a cikin azumin watan Ramadan.
Malam Jibrin Baba Ndace ya yi addu’ar Allah ya karawa ‘yan Najeriya farin ciki da walwala, da kuma sabon karfi domin su ci gaba da hada kai wajen samar da fahimtar juna, wajen bayar da gudunmawa mai kyau ga ci gaba da zaman lafiyar Nijeriya.
PR ALIYU LAWAL