Yau Litinin, ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar JKS ya kira wani taro na nazarin ayyukan kiyaye muhallin halittu, da rahoton ayyukan kewaye da kwamitin tsakiyar JKS karo na 20 ya gabatar, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jagoranci taron.

Taron ya nuna cewa, sa ido kan aikin kiyaye muhallin halittu wani muhimmin mataki a kokarin da kwamitin ya yi na kiyaye muhalli.

Dole ne a nace ga jagorancin da JKS ta bayar a wannan bangare, da ma sauke nauyin dake wuyan hukumomin wurare daban-daban karkashinta.

Taron ya kuma jadadda cewa, ya kamata a kara karfin sa ido a siyasance, da mai da hankali kan yadda ake tabbatar da manufofi da tsare-tsaren kwamitin, ta yadda za a ba da tabbaci ga aikin zamanintar da al’ummar Sinawa yadda ya kamata. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen jihar Filato ta gudanar da wata zanga-zangar lumana domin nuna adawa da matsalar tsaro da ke addabar jihar.

Zanga-zangar ta gudana ne makonni kaɗan bayan munanan hare-haren da aka kai a wasu ƙauyukan Bokkos da Mangu, waɗanda suka yi sanadiyyar aƙalla rayuka 100.

Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis

Waɗanda suka yi zanga-zangar sun haɗa da maza da mata da matasa har da tsofaffi ɗauke da alluna waɗanda aka rubuta wa saƙonni daban-daban.

Bayanai sun ce maƙasudin zanga-zangar ita ce kiran gwamnati kan ta ɗauki mataki kan kashe-kashen da ake yi a yankin.

Jihar Filato da wasu jihohin Arewa maso tsakiyar Nijeriya na ci gaba da fama da matsalar tsaro duk da matakan da hukumomi ke cewa suna ɗauka domin kawar da matsalar.

Rikici tsakanin manoma da makiyaya da kuma rikice-rikice masu alaƙa da bambancin addini da na ƙabila sun haifar da rasa rayukan ɗaruruwan mutane da tarwatsa wasu daga matsugunansu.

A makon da ya gabata ne gwamnan jihar Filaton, Caleb Manasseh Mutfwang ya sanar da ɗaukan wasu sabbin matakai na daƙile matsalar, ciki har da hana kiwon dare da kuma farfaɗo da ƙungiyoyin ’yan sintiri na sa-kai.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Aka Yi Zanga-zanga Kan Matsalar Tsaro A Filato
  • HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Ka Da Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
  • Kada Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?