Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
Published: 31st, March 2025 GMT
Mai martaba Sarkin Lere dake Kaduna Alhaji Sulaiman Umaru ya amince da nadin Sani Ahmed Lere Sardaunan Matasa zuwa Falakin Lere.
Hakan na kunshe ne a cikin takardar nadin da Sakataren Majalisar kuma Sadaukin Lere Alhaji Muhammad Lawal Ahmed ya sanya wa hannu.
Alhaji Muhammad Lawal Ahmed yace sabon nadin ya fara aiki ne nan take.
Ya bayyana cewa nadin Sani Ahmed Lere a matsayin Falakin Lere daga matsayinsa ne daga Sardaunan Matasan Lere wakilin Matasa a Masarautar zuwa Falakin Lere dan Majalisar Sarki kuma PPS ga Sarki.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarauta
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar CPPCC Ta Ziyarci Nijeriya Da Cote d’Ivoire Da Senegal
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp