Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya bayyana rashin jin daɗinsa dangane da kashe matafiya ’yan Arewa da aka yi a Jihar Edo.

Saboda haka Sarkin ya ce suna dakon ganin hukuncin da za a ɗauka dangane da faruwar wannan mummunan lamari.

Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka Dalilin da muka soke Hawan Bariki — Masarautar Zazzau

Da yake miƙa saƙon gaisuwar Sallah ga Gwamnan Sakkwato, Alhaji Ahmad Aliyu a ranar Litinin, Sarkin ya ce “mun ga an ɗauki mataki kan yanayin da ake ciki a Jihar Edo.

“Saboda haka muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka bayan kammala bincike don ba wani dalili ka kashe mutum ba tare da wani haƙƙi ba.

“Muna kiran jami’an tsaro da su tashi tsaye domin tabbatar da cewa jama’a ba su fusata ba sun ɗauki hukunci a hannunsu.

“Idan a wani wurin mutanen banza sun ɗauki hukunci a hannunsu, mu a nan Sakkwato ba za mu bari a yi abin da bai kamata ba.

“Mu sanya ’yan uwanmu da abin ya faru da su a cikin addu’a sannan muna kiran gwamnati da jami’an tsaro su ɗauki matakin kare rayukkan jama’a,” a cewar Sarkin Musulmi.

Sarkin ya ƙara da cewa “bai kamata a riƙa yaɗa abin da bai dace ba a kafafen sadarwa na zamani da za su janyo tashin hankali a wurin da ake da zaman lafiya.

“Duk wani abu da ya faru a wani wuri, bai kamata wasu da ke can wani wurin na daban su ce za su ɗauki mataki a Sakkwato ko Kano ko Kaduna kan wani abun da ya faru a Jihar Edo ko Legas ba.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano mafarauta Yan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar

“Mun zo nan ne a madadin gwamnatin tarayya domin ganowa da kuma jajanta muku rashin da aka yi, muna so mu tabbatar muku da cewa jami’an tsaro za su kawo karshen wannan kashe-kashen na rashin hankali.

 

“An yi mini cikakken bayani, kuma ina so in tabbatar muku cewa mun fahimci tushen wannan batu. Zamu kama wadanda suka aikata wannan aika-aika.

 

“Shugaban kasa ya damu matuka, kuma ya umarce mu da mu nemo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin su fuskanci shari’a, muna aiki tare da gwamnatin jihar domin daukar tsarin da zai hana faruwar wannan mummunan lamari, lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan hauka,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Wani Harin Amurka kan Yemen ya kashe fararen hula akalla 12
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?