A yau Litinin, hukuma mai kula da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin daga ketare, ta bayyana cewa, yanzu haka ana share fagen gudanar da bikin yadda ya kamata, inda yawan fadin shagunan da kamfanoni daban-daban suka kulla kwangilolin baje kolin kayayyakinsu a ciki ya kai muraba’in mita dubu 240, kuma ya kai 2/3 na fadin wurin da aka tanada.

Bikin nan da za a gudanar da shi a karo na 8, zai samu ci gaba a bangarori hudu. Na farko, za a tabbatar da fadin wurin bikin da ya kai muraba’in mita dubu 360, don baje kolin kayayyakin zamani. Na biyu, za a samar da dandaloli masu kyau ga mu’ammalar jami’an gwamnati da ‘yan kasuwa don kara hadin gwiwarsu. Na uku kuma akwai batun taimakawa matsakaita da kananan kamfanoni wajen kafa karin shirin tattalin arziki na yanar gizo, da makamashi masu tsafta da sauransu. Na hudu kuma, za a kara kokarin tabbatar da ingancin kayayyakin da ake shigar da su, da gayyatar karin kamfanoni a matakai daban-daban da su halarci bikin, ta yadda za a gaggauta samun daidaito tsakanin bukatun dake akwai da bangaren samar da kayayyaki. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe

Hatsarin mota ya yi ajalin mutum biyar tare da jikkatar wasu takwas a yayin da suke bikin Ista a garin Billiri da ke Jihar Gombe.

Hatsarin ya faru ne a safiyar ranar Litinin, lokacin da direban wata babbar mota mai ɗauke da buhunan hatsi daga Jihar Adamawa ya auka kan dandazon jama’a da ke tsaka da shagalin bikin Ista.

An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis An kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun yi gaggawar kai ɗauki, inda suka kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Sanarwar ta kuma ce bayan faruwar hatsarin, wasu fusatattun matasa sun cinna wa motar wuta tare da sace kayayyakin da ta ɗauko.

“Lokacin da ‘yan sanda suka kai ɗauki, matasan sun yi musu ruwan duwatsu, sai dai an shawo kan lamarin, kuma an dawo da zaman lafiya a yankin.”

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Gombe, Bello Yahaya, ya bayyana jimami kan faruwar lamarin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan.

Shi ma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayyana damuwa kan wannan iftila’i.

A cikin wata sanarwa da Babban Daraktan yada labarai na gidan gwamnati, Isma’ila Uba Misilli ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa lamarin abu ne mai girgiza zuciya.

Gwamnatin jihar ta yi alƙawarin ɗaukar nauyin magani ga waɗanda suka ji raunuka, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan kare faruwar irin wannan matsala a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Hukumar Kula Da Kasuwa: Adadin Kamfanoni Masu Zaman Kansu A Kasar Sin Ya Zarce Miliyan 57
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Kasar Rasha Ta Sanar Da Tsagaita Bude Wuta Da Ukraine Na Tsawon Kwanaki Bikin Ester
  • Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Duniya Ya Kara Fito Da Kyawun Kasuwar Sin
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa