Aminiya:
2025-04-22@12:05:20 GMT

Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari

Published: 1st, April 2025 GMT

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya yi kakkausan gargaɗi kan barazanar Amurka da ƙawayenta na kai wa ƙasarsa hari.

Khamenei ya sha alwashin maida mummunar martani idan har Amurka da ƙaddamar da hare-hare a ƙasar ta Iran.

Gargaɗin nasa martani ne kan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa ƙasar cewa za su kai mata hari.

Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka

“Suna yi min barazana, kuma idan suka sake suka kawo min hari tabbas zan rama,” in ji shi.

Yayin wata tattaunawa a ranar Asabar ne Trump ya yi alƙawarin kai wa Iran ɗin hari matuƙar ba ta amince da yarjejeniyar makamin ƙare dangin ba.

“Idan ba su amince da sabuwar yarjejeniyar makaman ƙare dangin ba, za mu tada bama-bamai,” in ji Trump.

Sai dai bai bayyana ko Amurkan ce za ta kai harin ba ko kuma ƙawarta Isra’ila.

To sai dai cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, kakakin ma’aikatar wajen Iran Esmaeil Baqaei ya ce barazanar ta Trump a bainar duniya yana matsayin shugaban kasa abin mamaki ne, kuma babbar barazana ce ga zaman lafiya da tsaron ƙasa da ƙasa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Iran

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tattaunawa da Amurka an yi ta ne cikin yanayi mai inganci da hangen nesa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana tattaunawar da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, wadda Oman ta shiga tsakani a birnin Roma na kasar Italiya, da cewa an gudanar da shi cikin yanayi mai ma’ana da hangen nesa.

A cikin wata sanarwa bayan tattaunawar, Araqchi ya yi nazari kan yanayin tattaunawar, inda ya bayyana cewa: “Sun gudanar da shawarwari na tsawon sa’o’i hudu a ci gaba da zaman da aka yi a baya, kuma sun samu kyakkyawar fahimta kan ka’idoji da manufofi da dama.”

Ya ci gaba da cewa: An amince da a ci gaba da tattaunawa, da shiga matakai na gaba, da fara taron kwararru. An shirya gudanar da tattaunawar fasaha a matakin kwararru a masarautar Oman daga ranar Larabar wannan makon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • Abubuwan da suka sa Fafaroma Francis ya yi fice a duniya
  • Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • News Fox: Sau 6  Yemen Ta Kakkabo Jiragen Amurka Samfurin Mq 9 A Karkashin Gwamnatin Trump