Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
Published: 1st, April 2025 GMT
Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya yi kakkausan gargaɗi kan barazanar Amurka da ƙawayenta na kai wa ƙasarsa hari.
Khamenei ya sha alwashin maida mummunar martani idan har Amurka da ƙaddamar da hare-hare a ƙasar ta Iran.
Gargaɗin nasa martani ne kan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa ƙasar cewa za su kai mata hari.
“Suna yi min barazana, kuma idan suka sake suka kawo min hari tabbas zan rama,” in ji shi.
Yayin wata tattaunawa a ranar Asabar ne Trump ya yi alƙawarin kai wa Iran ɗin hari matuƙar ba ta amince da yarjejeniyar makamin ƙare dangin ba.
“Idan ba su amince da sabuwar yarjejeniyar makaman ƙare dangin ba, za mu tada bama-bamai,” in ji Trump.
Sai dai bai bayyana ko Amurkan ce za ta kai harin ba ko kuma ƙawarta Isra’ila.
To sai dai cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, kakakin ma’aikatar wajen Iran Esmaeil Baqaei ya ce barazanar ta Trump a bainar duniya yana matsayin shugaban kasa abin mamaki ne, kuma babbar barazana ce ga zaman lafiya da tsaron ƙasa da ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ayatollah Ali Khamenei Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sari ya sanar da cewa sau uku su ka yi taho mu gama da sojojin da suke cikin jirgin dakon jirayen yakin Amurka “ Trauman” a cikin sa’oi 24.
A wata sanarwa da janar Yahya Sari ya yi a jiya Asabar ya bayyana cewa; Sun kai wa jirgin dakon jiragen yakin na Amurka da kuma sauran jiragen da suke ba shi kariya a cikin tekun “Red Sea”.
Kakakin sojan na kasar Yemen ya kuma ce; Sun kai wa jiragen na Amuka hare-hare ne da jiragen sama marasa matuki da kuma makamai masu linzami mabanbanta.
An shiga makwanni na uku kenan da sojojin na Yemen suke mayar da martani akan hare-haren da sojojin Amurka da Birtaniya suke kai wa kasarsu.
Kasar ta Yemen tab akin jagororinta za su ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare har zuwa lokacin da za a daina yaki da Gaza da kuma dauke takunkumin da aka akakaba wa zirin na hana shigar da kayan agaji.
Baya ga kai wa Amurka da Birtaniya da sojojin na Yemen suke yi, suna kuma hana duk wani jirgin ruwa ratsawa ta tekun “Red Sea” matukar zai nufi HKI.
Sa’o’i kadan da su ka gabata ma dai sojojin kasar ta Yemen sun harba makamai masu linzami zuwa HKI