Leadership News Hausa:
2025-04-22@18:00:12 GMT

Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Published: 1st, April 2025 GMT

Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Jamhuriyar Nijar ta ba da sanarwar ficewa daga Rundunar haɗin Kan Sojojin Kasashe Tafkin Chadi (MNJTF) da ke yaƙi da ta’addanci a yankin tafkin Chad. Sanarwar da aka fitar ta gidan talabijin na gwamnati kuma Reuters ta ruwaito, ta zo ne a lokacin da Nijar ke mai da hankali kan tsaron man fetur a cikin ƙasar, sakamakon tashin hankali na cikin gida.

Rundunar MNJTF, wadda ta ƙunshi Sojoji daga Najeriya, da Chadi, da Kamaru, da Nijar (a baya), an kafa ta ne a shekarar 1994 don magance barazanar tsaro a yankin. An sake farfaɗo da rundunar ne a shekarar 2014 domin yaki da Boko Haram, kuma ta taka muhimmiyar rawa a yaƙi da ta’addanci. Ficewar Nijar, wadda ta kasance muhimmiyar mamba, ya haifar da damuwa game da tasirin aikin rundunar, musamman yayin da ƙungiyoyin ta’addanci kamar Boko Haram da ISWAP ke ci gaba da yin barazana.

Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da Faransanci Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar

Shugabannin Soja na Nijar, waɗanda suka karbi mulki a shekarar 2023, sun ƙara nuna sabon tsarin tsaro na Kaɗaitaka bayan sun fice daga ECOWAS a shekarar 2024 tare da Burkina Faso da Mali. Ko da yake gwamnatin Nijar ta yi alƙawarin ƙarfafa tsaron cikin gida, har yanzu tana fuskantar ƙalubale, ciki har da hare-haren ‘yan ta’adda da barazana ga kayayyakin more rayuwa kamar bututun man fetur na Agadem.

Kawo yanzu, MNJTF ba ta yi magana kan ficewar Nijar ba, amma wannan yunƙuri na iya haifar da tasiri mai yawa kan yadda ake gudanar da yaƙi da ta’addanci a yankin Tekun Chad.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta

Brigadier General Ali Mohammad Naeini, kakakin dakarun dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar ya bayyana cewa dakarunsa a shirye suke fiye da ko wani lokaci wajen kara kan iyakokin JMI daga makami.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran Naeini yana fadar haka a yau Talata a wani taro da kafafen yada labarai a nan Tehran. Ya kuma kara da cewa a dai-dai lokacinda kasar ta cika shekaru 46 na nasarar juyin juya halin musulunci a kasar dakarun na IRGC suna cikin shirin da basu taba irinsa ba don kare kan iyakokin JMI.

Kafin haka, a farkon wannan watan jami’an gwamnatin JMI sun bayyana cewa kasar tana cikin shiri mai kyau na kare kan iyakokin kasar mai tsarki, sannan daga karshe sun bayyana cewa tsaron kasar jan layi ne ga makiya, don haka makiya sun yi hattara, kuma babu tattaunawa kan sa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Sin Na Hasashen Samun Karin Yabanya A Shekarar 2025
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 112
  • Fafaroma Francis ya Rasu
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan