HausaTv:
2025-04-02@14:37:46 GMT

HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari

Published: 1st, April 2025 GMT

Da safiyar Yau Talata jiragen yakin HKI sun kai hare-hare akan unguwar Dhahiya dake Beirut tare da bayyana cewa ta kai wa wani kusa ne a kungiyar Hizbullah hari.

Harin na yau shi ne irinsa na biyu da HKI ya kai a unguwar Dhahiya tun daga tsagaita wutar yaki a cikin watan Nuwamba na shekarar da ta gabata.

Jiragen yakin na HKI sun yi shawagi a kasa-kasan birnin Beirut kafin aji karar fashewar abubuwa masu karfi.

Kafafen watsa labarai sun ambaci cewa jiragen sun kai harin ne akan wani dogon gini a cikin unguwar.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa ya zuwa yanzu mutane 3 ne su ka yi shahada,yayin da wasu 4 su ka jikkata.

Masu ayyukan ceto sun nufi wurin da aka hai harin, domin daukar wadanda su ka jikkata zuwa abitocin da suke kusa.

Jotunan farko sun nuna yadda gine-ginen da suke yankin su ka illata, biyu daga cikinsu sun rushe baki daya.

Mazauna yankin sun ce, an kai harin ne a lokacin da mutane suke bacci, lamarin da ya haifar da firgici a tsakaninsu.

A ranar Asabar din da ta gabata dai babban magatakardar kungiyar Hizbulllah Sheikh Na’im Kassim ya yi gargadin cewa, Idan HKI ta ci gaba da keta yarjeniyar tsagaita wuta, sannan kuma ba a taka mata birki ba, to suna da zabin abinda za su yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci

Wani basakkwace, Musa Abubakar, wanda a bayan nan ya yi ridda saboda zullumin ’yan bindiga masu kai hare-hare da ta’adar garkuwa da mutane, ya sake karɓar addinin Musulunci.

A ranar Asabar ce mutumin tare da matansa biyu suka sake karɓar addinin Islama bayan  ridda da suka yi a kwanan baya.

Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa

Bayanai sun ce Musa Abubakar ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Sakkwato ya yi ƙaura zuwa Jihar Taraba a sakamakon yanayin tsaro a mazauninsa.

Bayan komawa Taraba ne kuma ya shawarci matansa uku da su  karɓi addini Kiristanci, kuma ya yi nasara biyu suka amince.

Sai dai wannan lamari ya tayar da ƙura musamman a Sakkwato, inda har ta kai ga Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya haɗa kwamitin malamai domin su faɗakar da Musa kan ridda da ya yi.

Aminiya ta ruwaito cewa mambobin kwamitin sun haɗa da Alƙalin Alƙalai na Sakkwato, Malam Ahmad Umar Helele da Sarkin Malamai, Malam Yahya Na-Malam da kuma Malam Bashir Gidan Kanawa a matsayin sakataren kwamitin.

A yayin ganawa da mambobin kwamitin, Musa Abubakar ya shaida musu dalilan da suka fusata shi ya yi ridda ya koma Kirista.

Da yake zantawa da manema labarai kan binciken kwamitin, Malam Gidan Kanawa ya bayyana cewa, Musa Abubakar yana da ƙarancin ilimin addini baya ga rasa sana’arsa da ta’addancin ’yan bindiga ya haddasa.

“Wannan lamari ne ya fusata shi, ya jefa shi cikin ƙuncin rayuwa kuma ya yanke shawarar ƙaura zuwa Taraba, inda a nan aka yi amfani da tallafin kuɗi wajen kwaɗaita masa shiga Kiristanci,” in ji shi.

Da yake bayyana halin da shiga, Musa Abubakar ya ce ya yi ridda ne watanni kaɗan da suka gabata, amma a yanzu ya sake karɓar addinin Islama a sakamakon faɗin tashin da ’yan uwansa da malamai da shugabanni suka yi.

“A yanzu na dawo na karɓi addina na Islama tare da iyalina. Na yi nadamar abin da na aikata da kuma damuwar da na jefa ’yan uwa da malamai.

“Yamzu ga ni na dawo Sakkwato kuma zan ci gaba da sana’a da sauran harkokin kasuwanci,” in ji Musa. Ya sha alwashin cewa shi da iyalansa za su sadaukar da rayuwarsu a kan addinin Islama. A nasa jawabin, wani yayan Musa Abubakar, Alhaji Adamu Sabon Birni, ya ce “ta’addancin ’yan bindiga masu garkuwa da mutane ne ya yi ajalin mahaifina.

“’Yan bindiga ne suka kashe shi bayan karɓa kuɗin fansa har Naira miliyan 9 amma hakan bai sa na yi ridda ba, saboda matsalar ta’addancin ’yan bindiga ba iya Sakkwato kaɗai ake fama da ita ba.

“A duk faɗin Arewa ana fuskantar wannan matsala kuma mahukunta na iya ƙoƙarinsu wajen magance ta.

“Saboda haka a yanzu muna farin ciki ya gane kuskuren da ya yi kuma ya sake karɓar addinin Musulunci.

Matan Musa Abubakar da aka zanta da su sun ce za su iya ƙoƙari wajen goyon bayan mijinsu don ganin ya ci gaba da zama a Sakkwato kuma ya dawwama a kan tafarkin addinin Islama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
  • Iran: Larijani Ya Ce Iran Zata Fara Kera Makaman Nukliya Idan An Kai Mata Hari Kan Shirin Ta Na Makamashin Nuliya
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  •  Larijani:  Dole Iran Ta Kera Makaman Nukiliya Idan Amurka Da Isra’ila Su Ka Kawo Ma Ta Hari
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Yawan Kayayyakin Da Aka Yi Hada-hadarsu A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Sin A 2024 Ya Ci Gaba Da Kasancewa Na Farko A Duniya
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Mutane Biyu Sun Mutu, 20 Sun Jikkata A Yamutsin Filin Idi A Gombe