Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@15:49:58 GMT

BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa

Published: 1st, April 2025 GMT

BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta kaddamar da wani tsari na yanar gizo wanda zai baiwa dalibai damar shiga da duba sakamakon kammala karatunsu ta hanyar lambobi.

 

Wannan sabon yunkuri shine karo na farko da cibiyar ta samar da sakamako ta hanyar irin wannan dandali.

 

An sanar da shirin ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun mataimakin magatakarda kuma shugaban hukumar kula da harkokin jama’a Lamara Garba Azare.

 

A cewar sanarwar jami’ar, tsarin da myBUK Team ya kirkira kuma yana bawa ɗalibai damar dawo da sakamako kai tsaye ta hanyar amfani da sashen rajistar dalibai.

 

Takardun sakamakon za su nuna a sarari na kowane kwasa amma dole ne ɗaliban da suka kammala shekarar ƙarshe su jira amincewar Majalisar Dattawa kafin su sami sakamakonsu.

 

Daya daga cikin shugabannin kungiyar dalibai a Jami’ar, Bilal Muhammad Bello, ya yabawa ci gaban da aka dade ana jira tare da bada tabbacin cewa wannan zai rage damuwar dalibai da kuma kawar da jinkiri da aka samu wajen samun sakamakon.”

 

“Wannan tsarin yana ba ɗalibai damar sanya ido kan ci gaban karatun su tare da kawar da cunkoson da ake samu na jama’a a a allon manna sakamakon jarabawa.”

 

Da yake tsokaci kan zaman sa a matsayin Sanata na 24 na SUG mai wakiltar Sashen Sadarwa, Bello ya ce. “Na ba da shawarar samun damar samun sakamako ta yanar gizo a lokacin da nake majalisar dalibai, Alhamdulillah, wannan hangen nesa ya zama gaskiya.”

 

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki

Ya ce, bisa tagomashin katafariyar kasuwarta, da kyawawan manufofin da ake tsammani, da ingantaccen yanayin kasuwanci, Sin na ci gaba da zama kasa mai albarka ga kamfanonin kasa da kasa su zo su zuba jari domin samun bunkasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga, Sun Ceto Ɗalibai 2 A Nasarawa
  • Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus
  • Kasar Sin Mai Tabbatar Da Daidaito A Duniya Mai Cike Da Rashin Tabbas
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • BUK Ta Ƙaddamar Da Shafin Intanet Da Ɗalibai Za Su Ke Duba Sakamakon Jarrabawa
  • Nigeria: Zazzabin “Lassa” Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 118 Tun Farkon Wannan Shekara
  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5