Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-22@16:04:40 GMT

BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa

Published: 1st, April 2025 GMT

BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta kaddamar da wani tsari na yanar gizo wanda zai baiwa dalibai damar shiga da duba sakamakon kammala karatunsu ta hanyar lambobi.

 

Wannan sabon yunkuri shine karo na farko da cibiyar ta samar da sakamako ta hanyar irin wannan dandali.

 

An sanar da shirin ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun mataimakin magatakarda kuma shugaban hukumar kula da harkokin jama’a Lamara Garba Azare.

 

A cewar sanarwar jami’ar, tsarin da myBUK Team ya kirkira kuma yana bawa ɗalibai damar dawo da sakamako kai tsaye ta hanyar amfani da sashen rajistar dalibai.

 

Takardun sakamakon za su nuna a sarari na kowane kwasa amma dole ne ɗaliban da suka kammala shekarar ƙarshe su jira amincewar Majalisar Dattawa kafin su sami sakamakonsu.

 

Daya daga cikin shugabannin kungiyar dalibai a Jami’ar, Bilal Muhammad Bello, ya yabawa ci gaban da aka dade ana jira tare da bada tabbacin cewa wannan zai rage damuwar dalibai da kuma kawar da jinkiri da aka samu wajen samun sakamakon.”

 

“Wannan tsarin yana ba ɗalibai damar sanya ido kan ci gaban karatun su tare da kawar da cunkoson da ake samu na jama’a a a allon manna sakamakon jarabawa.”

 

Da yake tsokaci kan zaman sa a matsayin Sanata na 24 na SUG mai wakiltar Sashen Sadarwa, Bello ya ce. “Na ba da shawarar samun damar samun sakamako ta yanar gizo a lokacin da nake majalisar dalibai, Alhamdulillah, wannan hangen nesa ya zama gaskiya.”

 

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho

Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna ta hanyar wayar tarho da takwarorinsa na Switzerland da Pakistan

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi wata ganawa ta hanyar wayar tarho guda biyu a yammacin jiya Lahadi tare da ministocin harkokin wajen kasashen Switzerland da Pakistan.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gana da ministan harkokin wajen kasar Switzerland Ignazio Cassis ta hanyar wayar tarho a yammacin jiya Lahadi, inda suka tattauna kan alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kuma wasu batutuwan kasa da kasa tare da yin musayar ra’ayi a kansu.

A yayin wannan tattaunawa, ministan harkokin wajen na Iran ya bayyana jin dadinsa ga rawar da kasar Switzerland ta taka a shawarwarin nukiliyar kasar cikin shekaru 10 da suka gabata, tare da bayyana wa takwaransa na kasar Switzerland sabbin ci gaba da suka shafi tattaunawar da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Burnley Da Leeds United Sun Dawo Gasar Firimiya Lig 
  • Sin Na Hasashen Samun Karin Yabanya A Shekarar 2025
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sabuwar Cibiyar Sayar Da Magunguna Da Ke Damaturu
  • Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
  • Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango