Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@15:52:20 GMT

Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe

Published: 1st, April 2025 GMT

Gwamna Edo Okpebholor Ya Jajantawa Iyalan Wadanda Aka Kashe

Game da aka yi wa mafarauta 16 a Udune Efandion, karamar hukumar Uromi ta jihar Edo, gwamna Monday Okpebholo ya yi kakkausar suka ga wannan aika-aika na rashin hankali, yana mai bayyana hakan a matsayin “wani abu da kuma muguwar dabi’a.

 

 

Okpebholo, tare da Gwamna Abdullahi Yusuf na Jihar Kano, sun yi addu’a ga rayukan wadanda abin ya shafa a kauyen Bunkure na jihar Kano inda wadanda abin ya shafa suka fita tare da kuma da bada tabbacin ga iyalan wadanda abin ya shafa cewa za a gurfanar da masu laifin gaban kuliya.

 

Allah wadai da gwamnan ya biyo bayan harin da wasu gungun ’yan bindiga suka kai wa mafarautan, wadanda aka yi kuskuren cewa masu garkuwa da mutane ne, wanda ya yi sanadin kashe mutane 16.

 

 

Lamarin dai ya janyo cece-ku-ce, inda shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a farauto wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da umurtar jami’an tsaro da su gudanar da bincike cikin gaggawa.

 

Okpebholo ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa za ta dauki dukkan matakan da suka dace domin ganin an kamo duk wanda ke da hannu a harin tare da gurfanar da shi gaban kuliya. Ya zuwa yanzu dai an kama mutane 14 da ake zargi da hannu a lamarin.

 

Gwamnan ya kuma yabawa al’ummar jihar Kano da ma daukacin yankin Arewa kan rashin daukar doka a hannunsu da sunan harin ramuwar gayya.

 

 

Ya sanar da cewa, ana shirin bayar da diyya ga duk wadanda lamarin ya shafa.

 

Gwamna Yusuf wanda ya karbi bakuncin Okpebolo a Kano, ya yi alkawarin bayar da tallafin kudi da kayan abinci ga iyalan mafarauta da aka kashe a Uromi, jihar Edo.

 

 

Ya kuma yi alkawarin cewa za a biya diyya ga wadanda lamarin ya shafa, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wadanda abin ya shafa

এছাড়াও পড়ুন:

An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su

Mai martaba Sarkin zazzau,kuma shugaban majalisar sarakunan jihar kaduna, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bukaci Dagatan da ke masarautar zazzau da su rinka sanya ido sosai akan zirga-zirgar bakin fuskokin da ba su gane ba a cikin su.

Ya yi kiran ne a sakon sa na sallah bayan kammala azumin watan Ramadan a fadar sa dake Zaria.

Ahmed Nuhu Bamalli ya bayyana cewa harkar tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a hakki ne na kowa amma ba gwamnati ita kadai ba,a don haka akwai bukatar ganin an hada karfi da karfe domin samun nasara a game da tsaron.

Mai martaba Sarkin ya kuma bukaci Dagatan da su rinka kai rahoton zuwan duk wani bako ko bakuwa da kuma dalilin zuwan.

Ya ce idan har aka dauki wannan matakin matsalar tsaro za ta ragu sosai,yana mai nuni da cewa sarakunan gargajiya na da muhimman rawar da za su taka game da tsaro.

Haka kuma Sarkin na zazzau ya bukaci iyaye da su rinka sanya ido game da harkokin yau da kullum na ‘ya’yan su.

Haka kuma ya gode wa gwamnan jihar kaduna da shugaban majalisar wakilai,Dr Abbas Tajuddeen, Iyan zazzau saboda irin aiyukan ci gaban da suke samar wa talakawa a zaria da sauran kananan hukumomin jihar kaduna.

A wani labarin kuma,Limamin masallacin juma’a na rukunin kananan gidajen dake kofar Gayan,Zaria, Sheikh Dalhatu Bello Amaru ya yi Allah wadai da kisar Gilla da wasu yan ta’adda suka yi wa wasu mafarauta yan arewa su 11 a Uromi da ke jihar Edo.

Ya yi Allah wadan ne a hudubar sa ta sallar idin karamar sallah da ya gudanar.

Ya ce mutanen Arewa ba su amince da kisar gillar da aka yi wa maharban ba gaira ba dalili.

Sheikh Bello Amaru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Edo da su tabbatar da ganin an kamo duk mutanen da suka aikata laifin domin suma a kashe su domin ran su bai fi na mafarautar da suka kashe ba tare da wani dalili ba.

Ya yi Bayanin cewa Allah ya bada umurnin cewa duk wanda ya kashe wani shima a kashe shi,amma hakan bai bada damar wani ya dsuki doka a hannun shi ba,hakki ne na hukumomin da abin ya shafa.

Haliru Hamza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Edo Za Ta Biya Diyyar Mafarauta ‘Yan Kano 16 Da Aka Kashe A Uromi 
  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Gwamna Abba ziyarar barka da Sallah
  • HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su