HausaTv:
2025-04-02@17:41:03 GMT

Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji

Published: 1st, April 2025 GMT

Jami’an tsaro sun bazama akan titunan manyan garuruwan kasar Zimbabwe domin dakile zanga-zangar da ake shirin yi domin yin kira ga shugaban kasa Emmerson Mnangagwa ya yi murabus.

Tsofaffon sojoji da mayakan da su ka samarwa kasar ‘yanci ne dai suka yi kiran a yi zanga-zangar, saboda kin amincewa da shirin shugaban kasar na tsawaita wa’adin mulkinsa.

A cikin watan Janairu na wannan shekarar ne dai jam’iyyar ZANU-Party, mai mulki a kasar ta sanar  da cewa tana son Mnangagwa ya ci gaba da rike mukamin shugaban kasar har zuwa 2023.

Mnangagwa dai ya hau karagar mulkin kasar ta Zimbabwe ne tun a 2017,bayan sauke Robert Mugabe daga kan karagar mulki cikin ruwan sanyi.

Shugaban mayakan nemawa kasar ‘yanci Blessed Geza ya zargi shugaban kasar da cin hanci da rashawa da kuma yi wa kujerar mulki rikon danko.

Shugaban kasar ta Zimbabwe dai ya sha bayyana cewa, ba ya da nufin tsawaita lokacin shugabancinsa.

Kundin tsarin mulkin Zimbabwe wanda aka rubuta a 2013 ya kayyade wa’adin shugabancin kasar na shekaru biyar sau biyu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba

Shugaban majalisar mulkin kasar Sudan kuma kwamandan Sojin kasar Abdel Fattah al-Burhan ya tabbatar da cewa, farin cikin samun nasara a Sudan ba zai cika ba har sai an kawar da tungar karshe ta mayakan RSF a kasar, yana mai jaddada cewa kasar ba za ta ja da baya ba har sai an murkushe wadannan mayakan ‘yan tawaye, wadanda suka aikata munanan laifuka kan al’ummar Sudan.

Al-Burhan ya yi nuni da cewa, za a ci gaba da gwabzawa har sai an samu cikakken adalci, yayin da ya tabbatar da cewa ya tsaya tsayin daka da dukkan ‘yan kasar, kuma ya yi imani da ci gaba da kokarin maido da tsaro da kwanciyar hankali a kowane sako  na kasar Sudan.

Al-Burhan ya ce: Har yanzu hanyar zaman lafiya da kawo karshen yakin a bude take, kuma duk wannan abu ne mai yiyuwa, kuma hanya a fili take, wato kungiyar RSF ta ajiye makamanta.

Ya tabbatar da cewa babu wata niyya ta tattaunawa da Rundunar ta RSF a yanzu, inda ya bayyana cewa kofar yin afuwa a bude take ga duk wanda ya ajiye makamansa. A ranar Asabar din da ta gabata ce sojojin kasar Sudan suka sake karbe ikon Kasuwar Libiya da ke yammacin birnin Omdurman, lamarin da ke nuna wani gagarumin mataki na ci gaba da suke samu, wanda ya biyo bayan sake kwac fadar shugaban kasa daga hannun dakarun RSF da sojojin na Sudan suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mu Leka Shirin “Bunkasa Tagomashin Kirkirarriyar Basira Ta AI” Na Kasar Sin
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Iran: Larijani Ya Ce Iran Zata Fara Kera Makaman Nukliya Idan An Kai Mata Hari Kan Shirin Ta Na Makamashin Nuliya
  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPC
  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba