Cibiyar da take dakile yaduwar cutuka masu yaduwa ( NCDC) ta sanar a ranar Lahadin da ta wuce cewa, a kalla mutane 118 ne su ka rasa rayukansu sanadiyar yaduwar zazzabin Lassa tun daga farkon wannan shekara ta 2025.

A wata sanarwar da cibiyar ta fitar ta bayyana cewa; An sami yaduwar wannan cuta a cikin jahoji 33 na fadin kasar, kuma bincike da aka yi akan wadanda ake tsammanin ta kama, ya tabbatar da cewa an sami mutane 645 da su ka kamu da ita.

Ita dai wannan cutar mai yaduwa a Nigeria, ana kamuwa da ita ne ta hanyar cudanya a tsakanin mutane ko kuma taba kayan gida da su ka gurbana daga bahaya ko fitsari na mutane da su ka kamu da ita.

Tare da cewa an dauki shekara da shekaru ana fama da wannan cutar a cikin kasar ta Nigeria, sai dai har yanzu babu wani ci gaba na azo a gani da aka samu na dakile wannan cuta, saboda halayyar kazanta da rashin muhalli mai tsafta.

Ana samu wadanda suke tsira daga cutar amma a lokaci daya tana kisa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

**Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba

Hukumar lura da gidajen bashin ma’aikatan gwamnatin tarayya (FGSHLB) ta sanar da cewa ta fara tattara jerin sunayen ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya amma ba su biya bashin gidajen da suka karɓa ba.

Shugabar sashin sadarwa da hulɗa da jama’a na FGSHLB, Ngozi Obiechina, ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis a Abuja, inda ta ruwaito cewa shugabar hukumar, Salamatu Ahmed, tana cewa wannan matakin yana nufin dawo da dukiyoyin da aka yi rance daga ma’aikatan da suka yi ritaya amma ba su kammala biyan bashin ba.

Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya: Jigon Ziyarar Xi A Kudu Maso Gabashin Asiya

Salamatu Ahmed, ta bayyana cewa wannan hukuncin ya biyo bayan wanta takardar saƙo da sakatariyar dindindin ta ofishin gudanar da ayyukan ma’aikatan gwamnati, Patience Oyekunle, ta fitar. Ta ce takardar ta tunatar da ma’aikatan gwamnati kan bukatar samun takardar shaidar bashi da ba a biya ba daga FGSHLB da MDA Staff Multipurpose Cooperative Society a matsayin sharadi na yin ritaya, tana mai cewa hukumar za ta dauki matakai na shari’a don dawo da dukiyoyin idan an samu da wasu da karya yarjejeniyar bashin.

Ta kuma kara da cewa wannan matakin yana cikin ka’idojin dokokin ayyukan gwamnati na 021002 (p) da Ofishin shugaban ma’aikatan gwamnati na tarayya ya fitar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Damƙe Mutane 148, Sun Ƙwato Makamai A Adamawa
  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Burkina Faso ta sanar da dakile wani yunkurin juyin mulkin a kasar
  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Siyasantar Da Batun Asalin Cutar COVID-19 
  • Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel