Wasu gidajen na ‘yan kasuwa ma sun bi sahu wajen ƙara farashi, wanda hakan ya ƙara jefa ‘yan Nijeriya cikin matsin tattalin arziƙi.

A halin yanzu, hauhawar farashin man fetur na nufin za a ƙara kudin sufuri da kuma farashin kayan masarufi, wanda zai ƙara jefa al’umma cikin kunci.

Masana harkar man fetur sun yi gargaɗin cewa, idan ba a magance rikicin da wuri ba, farashin mai na iya haura Naira 1,000 a wasu yankuna.

Gwamnatin Tarayya ta taɓa bayar da umarni cewa a sayar da ɗanyen mai ga matatun cikin gida da Naira domin daidaita farashin mai, amma yarjejeniyar ta ƙare a watan Maris 2025.

A halin yanzu, ana ci gaba da tattaunawa kan sabuwar yarjejeniya.

A yayin da wannan rikici ke ci gaba, ‘yan Nijeriya na fama da illolinsa.

An fara samun dogayen layukan a wasu yankuna a gidajen mai, sannan ‘yan kasuwa da ke amfani da janareta don samar da wutar lantarki na ƙara kokawa kan tsadar man.

Mutane da dama na kira ga gwamnati da ta gaggauta ɗaukar mataki domin shawo kan matsalar kafin ta ƙara ta’azzara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Farashi

এছাড়াও পড়ুন:

Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta

Kasashen Indiya da Pakistan sun tabbatar da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bayan shafe kwanaki suna yi wa juna luguden wuta da makaman atilare.

Shugaban Amurka Donald Trump ne ya sanar da cewa ƙasashen biyu maƙwabta sun amince su cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta nan take bayan shafe dare guda ana tattaunawa.

Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina

“Bayan doguwar tattaunawa da Amurka ta yi na a cikin dare, ina farin cikin sanar da cewa Indiya da Pakistan sun amince da tsagaita wuta cikin gaggawa.

“Ina taya ƙasashen biyu murna a kan amfani da hankalinsu da kuma basira,” kamar yadda Trump ɗin ya bayyana a shafinsa na Truth Social.

Shi ma Ministan Harkokin Wajen Pakistan Ishaq Dar ya tabbatar da maganar Trump ɗin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce “Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta da gaggawa. Pakistan a ko da yaushe tana kokarin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, ba tare da ƙasa a gwiwa kan ƙarfin ikonta da maratabar ƙasarta ba!

Ita ma Ma’aikatar Harkokin Wajen Indiya ta tabbatar da batun tsagaita wutar inda ta ce yarjejeniyar za ta fara aiki ne a ranar Asabar da misalin 1700 agogon Istanbul.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Indiya da Pakistan sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Jagora Ya Jaddada Wajabci Daukan Matakan Kalubalantar Zaluncin ‘Yan Sahayoniyya
  • Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama
  • Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
  • Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
  • Iran Zata Fara Aikin Nema Da  Kuma Hakar Danyen Man Fetur A Cikin Ruwan Tekun Caspian
  • JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025
  • AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
  • Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
  • An Bude Kasuwar Baje Koli Na Man Fetur Da Gas Karo Na 29 A Nan Tehran