Aminiya:
2025-04-02@17:37:09 GMT

Gangamin da zan yi a mazaɓata babu fashi — Natasha

Published: 1st, April 2025 GMT

Sanata Natasha Akpoti wadda a kwanan nan Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar na tsawon watanni shida, ta ce “babu gudu babu ja da baya dangane da gangamin gaisuwar Sallah” da ta shirya yi a mazaɓarta.

Hakan na kunshe ne cikin wani sakon mayar da martani da Sanata Natasha ta wallafa a shafinta na Facebook.

Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda HOTUNA: Abba da Gwamnan Edo sun ziyarci iyalan mafarautan da aka kashe a Edo

Ta bayyana cewa “babu gudu babu ja da baya dangane da wannan gangamin na Sallah.

Ta yi zargin cewa duk wani abu da ya faru za ta ɗora alhakinsa ne a kan Gwamna jihar, Ahmed Usman Ododo da tsohon gwamnan jihar, Yahaya Bello da kuma Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

“Kuma duk abin da ya same mu to za mu ɗora alhakin ne kan gwamnan jihar, Ahmed Usman Ododo, Yahaya Bello da Godswill Akpabio,” a cewar saƙon.

Wannan na zuwa ne bayan da rundunar ’yan sandan Jihar Kogi ta nemi Sanata Natasha ta jingine shirinta na kai ziyara da zummar hada gangamin bikin Sallah a jihar.

Wata sanarwa da kakakin ’yan sandan Jihar Kogi, ASP William Aya ya fitar, ta ambato Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP William Ɗantawaye na cewa gangamin ya ci karo da haramcin gudanar da gangamin siyasa da gwamnatin jihar ta yi ranar Litinin.

A sakamakon rahoton sirri kan barazanar tsaro a jihar Kogi da ya sanya hana duk wani gangami da jerin gwano da gwamnatin jihar Kogi ta yi, rundunar ‘yan sandan na kira ga wadanda suka shirya gangamin a Okene da su jingine irin wannan taron domin samar da zaman lafiya a Jihar Kogi.

Sanarwar ta ce, “kiran a jingine gangamin ya zama dole ne bisa rahotannin sirri da muka samu dangane da ƙoƙarin wasu ɓata gari na karkatar da gangamin zuwa wani abu daban da ka iya jefa jihar cikin tashin hankali.

“Saboda haka rundunar ’yan sandan ba za ta zura ido ta bar duk wani abun da zai jefa jihar mai zaman lafiya zuwa tashin hankali ba,” in ji sanarwar.

A watan da ya gabata ne dai zauren Majalisar Dattawan Nijeriya ya dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan bisa zargin rashin da’a, kan sauya mata matsugunni da ta ce an yi ne ba bisa ka’ida ba kuma tta alakanta shi da zargin da take yi wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio da cin zarafi da neman ta da lalata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gangamin Siyasa Jihar Kogi

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano

Rundunar ’Yan Sandan Kano, ta kama wani matashi bisa zargin kashe jami’in tsaron sa-kai a filin Idi yayin hawan sallah ƙarama.

A cewar sanarwar da ’yan sanda suka fitar, matashin mai shekara 20, ya daɓa wa jami’in wuƙa yayin da yake aiki tare da tawagar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, bayan sallar Idi a ranar Lahadi.

Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Haka kuma, wani jami’in sa-kai ma ya ji rauni kuma yana jinya a Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano.

Rundunar ’yan sandan ta ce ta fara bincike kan lamarin, kuma ta gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin amsa tambayoyi.

A baya-bayan nan, ’yan sanda sun hana gudanar da Hawan Sallah a Kano, yayin da ake ci gaba da rikicin sarauta tsakanin Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda
  • Sanata Yari Zai Tallafa Wa Marayu 20,000 A Zamfara
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar