Aminiya:
2025-04-23@19:25:49 GMT

HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Gwamna Abba ziyarar barka da Sallah

Published: 1st, April 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya karɓi baƙuncin Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, a fadar gwamnatin jihar.

Sarkin dai ya kai wa gwamnan ziyarar ce kamar yadda aka saba a Hawan Nassarawa da ake gudanarwa bisa al’ada duk shekara.

Sai dai a sakamakon haramcin gudanar da haye-hayen sallah da rundunar ’yan sandan jihar ta yi, Sarkin bai cika duk tsare-tsaren da al’ada ta tanada ba na gudanar da Hawan Sallah.

Aminiya ta ruwaito cewa, Sarkin wanda ya yi ƙoƙarin kawar da idon jama’a, ya bi ta wasu hanyoyin da ba su aka saba bi wajen kai wa gwamna ziyara a yayin gudanar da hawan cikakke.

Haka kuma, Sarkin ya yi amfani da jerin gwanon motoci ƙalilan maimaiko hawa dawakai

Sai dai an tsananta tsaro a duk hanyoyin da Sarkin ya bi tun daga Fadar Sarki ta Gidan Ƙofar har zuwa Gidan Gwamnatin Kano.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Nasarawa Jihar Kano Sarki Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano

Janar Tukur ya yaba wa sojojin bisa jajircewa da kwarewa da suka nuna a yayin aikin, wanda ya kai ga kwato tarin makamai da alburusai da sauran su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa
  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Matashin Da Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kano
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • HOTUNA: Pantami ya kai wa Sheikh Jingir ziyarar ta’aziyya
  • HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sashen Koyar Da Kwararrun Likitoci A Damaturu
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sabuwar Cibiyar Sayar Da Magunguna Da Ke Damaturu
  • Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.