Aminiya:
2025-04-23@01:07:12 GMT

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola

Published: 1st, April 2025 GMT

Kociyan Manchester City, Pep Guardiola, ya ce ɗan wasan gaban ƙungiyar, Erling Haaland, zai yi jinyar mako bakwai a sakamakon raunin da ya samu a idon sahunsa a wasan kofin FA da ƙungiyar ta fafata da Bournemouth a ranar Lahadi.

Ɗan wasan na ƙasar Norway bai ƙarasa wasan ba, inda aka cire shi a minti 61 da fara wasan bayan ya farke ƙwallo ɗaya, kafin daga bisani City ta doke Bournemouth da ci biyu da ɗaya domin zuwa wasan kusa da na ƙarshe.

HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah Gangamin da zan yi a mazaɓata babu fashi — Natasha

Tun a jiya Litinin ce City ta ce Haaland zai ga ƙwararren likita saboda raunin da ya ji rauni, kuma tana sa ran zai warware ya ci gaba da taka leda a wannan kakar da ake ciki.

Sai dai a yau Talata gabanin wasan da City za ta fafata da Leicester City a Firimiyar Ingila, Guardiola ya sanar da cewa likitocin sun tabbatar da cewa ɗan wasan zai yi jinyar mako biyar zuwa bakwai kafin ya iya dawowa taka leda a Etihad.

A bayan nan dai City na fuskantar cakwakwiyar ’yan wasa da ke fama da jinya, ciki har da Rodri wanda ya lashe kambun gwarzon ɗan wasa ta Balon d’Or a bara.

A yanzu dai City ba ta wani ɗan wasa da zai iya maye gurbin Haaland, amma Guardiola ya ce ƙungiyar za ta ƙarasa kakar wasannin a daddafe a haka kuma za ta jajirce don samun gurbin zuwa Gasar Zakarun Turai mai zuwa.

A halin yanzu City mai maki 48 na mataki na biyar a teburin Firimiyar Ingila yayin da ya rage mata wasanni tara da kuma wasan mataki na biyun ƙarshe a Kofin FA da za ta kece raini da Nottingham Forest a wannan wata na Afrilu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Erling Haaland Pep Guardiola

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu

Sahun farko na Alhazan Najeriya zai tashi zuwa kasa mai tsarki a ranar 9 ga watan Mayun 2025.

Hakan na kunshe ne a cikin bayanin bayan taro da Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON, ta yi da Shugabannin Hukomomin Kula da Jin Daɗin Alhazai na Jihohi a  ranar 22 ga watan Afrilun 2025.

Manufar taron ita ce tantance matakin shirin da kowace Hukumar Alhazai ta Jiha ta kai.

Wata sanarwa da mataimakiyar daraktar watsa labarai ta hukumar NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce shugaban hukumar, Farfesa Abdullah Saleh Usman, ya tunatar da mahalarta taron cewa harkar Hajji na cikin matakin karshe na shirye-shirye kafin fara aikin Hajjin shekarar 2025.

Ya bukaci jihohi da su sanar da NAHCON matsayin da suka kai wajen samar da biza, rigakafi, sayen jakunkuna da sauran batutuwa  da suka jibancu aikin hajji.

A yayin taron, Kwamishinan Ayyuka na NAHCON, Prince Anofiu Elegushi, ya bayyana cewa kamfanin Air Peace  zai yi jigilar alhazai 5,128 daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Rundunar Sojoji, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, da Taraba.

Yayin da kamfanin FlyNas zai dauki alhazai 12,506 daga Birnin Tarayya Abuja, Kebbi, Legas, Ogun, Osun, Sokoto da Zamfara. Kamfanin na FlyNas ya ware jirage tara domin gudanar da wannan aikin.

Sai kamfanin Max Air da zai dauki alhazai daga jihohin Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo da Filato.

Kamfanin na Max Air ya yi alkawarin kammala jigilar alhazai  15,203 zuwa ranar 24 ga Mayu, inda zai yi amfani da jirage biyu,  jirgin B747 mai daukar mutum 400, da wani mai daukar mutum 560.

Haka zalika, kamfanin Umza zai yi jigilar alhazai 10,163 daga jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Neja da Yobe. Shi kuma zai yi amfani da jiragin B747 mai daukar mutum 477 da B777 mai daukar mutum 310.

Wadanda kamfanonin jiragen sama 4 za su yi jigilar alhazan Hajjin 2025 su 43,000.

Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, Labarai da Ayyukan Laburare (PRSILS), Farfesa Abubakar Yagawal, ya bayyana wa mahalarta taron irin shirin da hukumar ta yi dangane da samar da asibitoci a Makka da Madina, rabon kati na Yellow Card ga jihohi, tare da tunatar da su da su guji yi wa mata masu ciki rijistar  aikin hajji.

Sanarwar ta kara da cewa yayin da aka cimma matsaya cewa ranar 9 ga Mayu za a fara tashi, ana kuma sa ran kammala jigilar a ranar 24 ga watan Mayu.

Har ila yau, sanarwar ta ce za a fara dawowa daga kasar mai tsarki a ranar 13 ga watan Yuni zuwa 2 ga watan Yuli, idan Allah ya yarda.

 

 

Safiyah Abdulkadir 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72
  • Yawan mutanen da aka kashe ya ƙari zuwa 72
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue