Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, a ranar Talata ya yaba wa Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano bisa bayar da fifiko akan ilimi, kiwon lafiya, noma, da tsaro a jihar. Sarki Sanusi II ya bayyana jin dadinsa ne a lokacin da ya kai gaisuwar Sallah ga gwamnan Kano, kamar yadda aka saba gudanarwa a al’adance duk shekara.

Sin Da Zambiya Sun Daddale Yarjejeniyar Fitar Da Kwarurun Macadamia Nuts Farashin Man Fetur Ya Ƙara Tashi Sakamakon Rikicin Dangote Da NNPCL “Mun zo ne domin mika gaisuwar mu ta barka da Sallah tare da gode muku bisa gagarumin aikin da kuke yi, musamman a fannin ilimi da noma, inda kuka samar da tallafin kayan aikin noma na zamani. “Muna godiya ga Allah da ya ba mu damar shaida wannan lokaci na musamman, inda muke taruwa don sake gaishe da Gwamna a yayin bikin Sallah,” in ji shi. Sanusi ya yabawa ‘yan majalisar dokokin jihar Kano bisa bin doka da oda da suka yi, wanda ya ce ya dawo da tsari da kimar masarautar. “Muna fatan gwamnan zai ci gaba da yin aiki mai kyau, kuma muna kira ga shugabannin kananan hukumomin da su yi koyi da shi, su kara kaimi,” in ji Sarkin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano

An yi jana’izar marigayi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi, a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda dubban jama’a suka halarta.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, sun halarci jana’izar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi.

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa

An gudanar da sallar jana’izar ne a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda Farfesa Sani Zahradden ya jagoranci sallar.

Dubban jama’a ne suka halarci jansiza5 marigayin.

Har ila yau, Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya halarci jana’izar.

Marigayi Alhaji Abbas Sunusi, ya rasu ne a daren ranar Talata a gidansa da ke Kano bayan doguwar jinya.

Ya rasu yana da shekara 92 a duniya.

An birne shi a makabartar Gandun Albasa.

Domin nuna alhini game da rasuwar marigayin, Gwamnatin Jihar Kano da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, sun dakatar da bukukuwan Sallar da suka shirya gudanarwa a yau Laraba.

Marigayi Galadima ya riƙe mukami mafi girma a Masarautar Kano, kuma shi ne mahaifin Abdullahi Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano.

Ga hotunan yadda jana’izar ta gudana:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi
  • Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano
  • Allah Ya Yi Wa Galadiman Kano, Abbas Sanusi, Rasuwa 
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah
  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Gwamna Abba ziyarar barka da Sallah
  • Muna kiran Natasha ta jingine gangamin da za ta yi a Kogi — ’Yan sanda
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama