Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
Published: 2nd, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya bayyana a yau Talata cewa, al’ummar Sinawa da ’yan kasar Rasha sun ba da gudummawa gaya wajen samun nasarar yakin duniya na biyu.
A wata hira da ya yi da rukunin gidajen rediyo da talabijin mallakin kasar Rasha wato Russia Today a yau a birnin Moscow, Wang ya bayyana cewa, bana shekara ce ta cika shekara 80 da samun nasarar yakin da Sinawa suka gwabza na tirjiya a kan zaluncin kasar Japan, da kazamin yakin kishin kasa na Tarayyar Soviet, da kuma yakin duniya na biyu.
Wang, ya yi kira ga kasashen biyu da su tsaya tsayin daka wajen tabbatar da adalci a matakin kasa da kasa yayin da ake fuskantar manyan sauye-sauyen da ba a taba ganin irinsu ba cikin karni guda a duniya, tare da hada karfi da dukkanin al’ummomin duniya masu son zaman lafiya, wajen kare tarihin da aka kafa ta hanyar zubar da jini da asarar rayuka, da kuma adawa da duk wani yunkuri ko mataki na musantawa, ko murgudawa, ko sake fasalin tarihin yakin duniya na biyu.
Ya bukaci kasashen biyu da su kiyaye tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin, da daukar bikin cika shekara 80 da kafa Majalisar Dinkin Duniya a matsayin wata dama ta tabbatar da iko da matsayin majalisar ta duniya, da aiwatar da hakikanin tsarin da ya kunshi bangarori daban-daban, da karfafa bin manufofi da ka’idojin yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya sau da kafa ga dukkan kasashe. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yakin duniya na biyu
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu na yau za yi magana dangane da “Rage kisasfin kudan ma’aikatar harkokin wajen Amurla da kimani kasha 50% da kuma tasirinsa ga matsayin Amurka a duniya da kuma cikin gida. Wanda ni tahir amin zan karanta.
A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan, rahe kasafin kudi na ma’aikatar harkokin wajen kasar da kasha 50%, saboda haka kuma ya rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancin kasar da kananan ofisoshin jakadancin kasar fiye da 30 a yankuna daban daban a duniya amma mafi yawansu a nahiyar Afirka.
Dangane da wannan matakin da gwamnatin kasar Amurka masana daga ciki ga wajen kasar ta Amurka masu yawa sun nuna damuwarsu da kuma rashin amincewarsu da hakan.
A majalisar dokokin kasar, wakilai daga jam’iyyu biyu masu mulkin Amurka wato Republican da kuma Democrat sun nuna rashin amincewarsu da matakan da shugaba Trump ya dauka, suna kuma ganin hakan wata alama ce jada bayan Amurka daga harkokin kasashen duniya, kuma da haka tauraron kasar zata dushe a duniya. Sannan akwai has ashen cewa kasar China zata maye gurbin Amurka a cikin al-amura da dama, musamman a kasashen da Amurka ta janye.
Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya janye kasar Amurka daga manya-manayn kungiyoyin bada agaji a duniya, wadanda suka hada da hukumar lafiya ta duniya WHO, hukumar abinci ta duniya.
Banda haka Amurka ta janye tallafin da take bawa kungiyar tsaro ta NATO wanda yake taimakawa abokan kasar na turai kan abubuwan da suka shafi tsaro, da kuma wasu al-amur da dama.
Masu sukan shugaban daga cikin har da sanatoci da tsoffin janar-janar na sojojin Amurla wadanda suka yi ritaya kimani 120 suke ganin, shugaban trump ya mikawa kasashen China da rasha dukkan wuraren da ya janye tallafi, ko kuma ya rufe ofishin jakadancin Amurka a duniya.
Wadannan masana dai suna ganin, ragewa ma’aikatar harkokin wajen kasar kudede masu yawa wanda ya kai dalar biliyon kimani 25, ya nuna cewa gwamnatin Amurka bata da wakilai a wasu wurare masu mihimmanci da dama a duniya, don haka ba zata sami labarin abinda yake faruwa a cikinsu ba. Kuma mai yuwa samun wadannan labarai suna da muhimmanci.
Wasu masu sukan suna ganin a halin da ake ciki mafi yawan kawayen Amurka, musamman kasashen turai sun tashi daga abokan aiki zuwa ga makiya ga gwamnatin Amurka. Sannan a kasashen masu tasowa, wadanda suke neman tallafi da taimako, Amurka ta bawa kasar China da Rasha dama ta su amfana da wadannan kasashe, ko basu bada kyauta ba, amma suna iya zuba jari a cikin kasashen inda bangarorin biyu zasu amfana.
A wani bangare kuma shugaban yana da shirin rage kudaden da ake kashewa ayyukan gwamnati a cikin gida, inda hakan ya kai ga rufe kafafen yada labarai da daman a gwamnatin Amurka. Hakan ya sa mutane da dama sun rasa ayyukansu a cikin kasar. Sannan daga kasashen waje ba, dubban ma’aikata sun rasa ayyukan daga kungiyoyin bada agaji ko kiwon lafiya ko tallafawa yara karkashin MDD wadanda gwamnatin Trump ta janye tallafin da suke bayarwa.
Daga karshe masana suna ganin, idan wannan halin ya ci gaba da alamun shugaba Donal Trump kama hanyar rusa kasar Amurka daga ciki da kuma wajen kasar a cikin shekaru 4 da zai yi a matsayin shugaban kasa. Mai yuwa gwamnatin da zata zo bayan tasa ta gaggauta gyaran wasu daga cikin abubuwan da ya bata. Amma wasu barnan da yayi ba zasu sake gyaruwa ba.
Don haka daga karshen dai Amurka ta kama hanyar wargajewa, idan ba an yi wani abu da gaggawa ba.