Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF
Published: 2nd, April 2025 GMT
Alƙaluman Asusun Tallafawa Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF ya ce Isra’ila ta kashe ƙananan yaran da yawansu ya kai 322 cikin kwanaki 10 da suka gabata a hare-haren da suke ci gaba da kai wa sassan Gaza.
Alƙaluman da UNICEF ta fitar ta ce a jimilla ƙananan yara fiye da dubu 15 ne Isra’ilan ta kashe cikin kusan watanni 18 da ta shafe tana yiwa yankin na Gaza luguden wuta, kuma daga lokacin da ƙasar ta katse yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninta da Hamas ta kashe ƙananan yaran da yawansu ya kai 322 tare da jikkata 609.
A cewar UNICEF galibin ƙananan yaran da Isra’ila ta kashe, na rayuwa ne a sansanonin wucin gadi bayan da hare-haren ƙasar ya rusa gidajensu tare da tilasta musu barin muhallansu.
Cikin adadin yaran har da tarin waɗanda Isra’ilan ta kashe suna tsaka da bukukuwan Sallah wato a ranar idi da washegari, galibinsu sanye da tufafi da kuma adon sallah kamar yadda hotuna suka nuna.
A cewar UNICEF yanzu haka akwai jumullar ƙananan yara fiye da dubu 34 da Isra’ilan ta jikkata, cikinsu har da waɗanda yanayi ke nuna yiwuwar sai an yanke musu wani sashe na jikinsu, a dai dai lokacin da ake fuskantar ƙarancin alluran kashe raɗaɗin ciwo a zirin na Gaza mai fuskantar ƙawanya.
Wannan alƙaluma na WHO na zuwa a daidai lokacin da Isra’ila ke amsa laifin cewa tabbas sojojinta ne suka buɗe wuta kan motar jami’an agaji kodayake Amurka ta ce laifin Hamas ne.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ƙananan yara da Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum ɗaya ya rasu, 3 sun jikkata a rikicin ’yan sara-suka a Filato
Wani rikici tsakanin matasan ƙungiyoyin Sara-Suka ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu uku a unguwar Yantifa da ke Jos ta Arewa, a Jihar Filato.
Shaidu sun ce matasan sun far wa juna da makamai irin su adduna, wanda ya sa mazauna yankin tserewa don tsira da rayukansu.
Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman KanoRikicin ya ɓarke ne a dare ranar Talata, lamarin da ya jefa jama’a cikin fargaba.
Lawan Chizo, wani jigo a ƙungiyar tsaro ta sa-kai, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya bayyana cewa sojoji da jami’an tsaro sun shiga tsakani don kwantar da tarzomar.
Ya ce rikicin ya haɗa da mambobin Sara-Suka daga Anguwan Rogo da Yantifa, waɗanda ke rikici da juna da daɗewa.
Duk da cewa har yanzu jama’a na cikin fargaba, Chizo ya tabbatar da cewa zaman lafiya ya wanzu a yankin.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, ya kira taron gaggawa tsakanin shugabannin al’ummomin yankin domin kawo ƙarshen rikicin.
Wannan rikici ya faru ne kwana biyu bayan wani faɗa da ya ɓarke a harabar Masallacin Al-Mohap, inda aka kashe mutum uku daga cikin ‘yan Sara-Suka.