A yau Talata, kasar Sin ta bayyana cewa, za ta dauki matakan ramuwar gayya domin mayar da martani game da sanarwar da Amurka ta fitar ta saka takunkumin biza a kan jami’an kasar Sin, bisa hujjar hana izinin shiga yankin Xizang mai cin gashin kansa, da ke kudu maso yammacin kasar Sin.

A yayin taron manema labarai da aka saba yi a-kai-a-kai, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana cewa, yankin Xizang a bude yake ga kowa da kowa, kuma ba a hana baki daga kasashen waje shiga ba, inda ya kara da cewa, yankin yana karbar dimbin matafiya da sauran al’ummomi da dama daga sassa daban-daban a kowace shekara, domin ko a shekarar 2024 kadai, akalla baki 320,000 ne suka shiga yankin.

Jami’in ya ce, kasar Sin tana kira ga Amurka da ta mutunta alkawuran da ta dauka kan batutuwan da suka shafi Xizang, da daina hada baki ko goyon bayan masu gwagwarmayar “’yancin kai” na Xizang, da kuma dakatar da amfani da batutuwan da suka shafi Xizang wajen yin katsalandan a harkokin cikin gidan kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka

Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da makamai masu linzami samfurin cruise a hare-haren da suka kai kan kataparen jirgin yaki mai daukarjiragen saman yaki na kasar Amurka da suke cikin tekun maliya a karo na ukku a cikin sa’o’ii 24 da suka gabata.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar sojojin kasar ta Yemen na fada a jiya Talata, kan cewa sun yi amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen saman yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa a wadan nan hare-hare kan USS Harry S.Truman kuma saun sami bararsu kamar yadda aka tsara.

Labarun ya kara da cewa yakin yana ci gaba tsakanin bangarorin biyu. Kuma wadan nan hare hare sun zo ne saboda maida martanin hare-haren da jiragen yakin Amurka suke ci gaba da kaiwa a kan kasar ta Yemen.

Majiyar ta kara da cewa hare-hare da makamai masi linzami kan HKI ma zai ci gaba kamar yadda gwamnatin kasar ta tsara.

Gwamnatin Amurka dai ta shiga yaki da sojojin Yemen ne saboda kare HKI a kan kissan kiyashin da takewa mutanen Gaza, sannan da kuma hana shigowar abinci da bukatun mutanen yankin tun fiye da wata guda da ya gabata. Har’ila yau sojojin Yemen sun hana jiragen ruwa kasuwanci na HKI ko wadanda suke zuwa can wucewa ta tekun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Daba Wa Kanta Wuka Bisa Karin Harajin Da Ta Yi 
  • Mutum ɗaya ya rasu, 3 sun jikkata a rikicin ’yan sara-suka a Filato
  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga, Sun Ceto Ɗalibai 2 A Nasarawa
  • Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin Matasa
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Sin Ta Gano Babban Yankin Hakar Danyen Mai A Tekun Kudancin Kasar
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran