Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci
Published: 2nd, April 2025 GMT
Wani basakkwace, Musa Abubakar, wanda a bayan nan ya yi ridda saboda zullumin ’yan bindiga masu kai hare-hare da ta’adar garkuwa da mutane, ya sake karɓar addinin Musulunci.
A ranar Asabar ce mutumin tare da matansa biyu suka sake karɓar addinin Islama bayan ridda da suka yi a kwanan baya.
Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa Kisan Mafarauta: Babu wanda aka kai wa harin ramuwar gayya a Kano — Ƙungiyoyin MatasaBayanai sun ce Musa Abubakar ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Sakkwato ya yi ƙaura zuwa Jihar Taraba a sakamakon yanayin tsaro a mazauninsa.
Bayan komawa Taraba ne kuma ya shawarci matansa uku da su karɓi addini Kiristanci, kuma ya yi nasara biyu suka amince.
Sai dai wannan lamari ya tayar da ƙura musamman a Sakkwato, inda har ta kai ga Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya haɗa kwamitin malamai domin su faɗakar da Musa kan ridda da ya yi.
Aminiya ta ruwaito cewa mambobin kwamitin sun haɗa da Alƙalin Alƙalai na Sakkwato, Malam Ahmad Umar Helele da Sarkin Malamai, Malam Yahya Na-Malam da kuma Malam Bashir Gidan Kanawa a matsayin sakataren kwamitin.
A yayin ganawa da mambobin kwamitin, Musa Abubakar ya shaida musu dalilan da suka fusata shi ya yi ridda ya koma Kirista.
Da yake zantawa da manema labarai kan binciken kwamitin, Malam Gidan Kanawa ya bayyana cewa, Musa Abubakar yana da ƙarancin ilimin addini baya ga rasa sana’arsa da ta’addancin ’yan bindiga ya haddasa.
“Wannan lamari ne ya fusata shi, ya jefa shi cikin ƙuncin rayuwa kuma ya yanke shawarar ƙaura zuwa Taraba, inda a nan aka yi amfani da tallafin kuɗi wajen kwaɗaita masa shiga Kiristanci,” in ji shi.
Da yake bayyana halin da shiga, Musa Abubakar ya ce ya yi ridda ne watanni kaɗan da suka gabata, amma a yanzu ya sake karɓar addinin Islama a sakamakon faɗin tashin da ’yan uwansa da malamai da shugabanni suka yi.
“A yanzu na dawo na karɓi addina na Islama tare da iyalina. Na yi nadamar abin da na aikata da kuma damuwar da na jefa ’yan uwa da malamai.
“Yamzu ga ni na dawo Sakkwato kuma zan ci gaba da sana’a da sauran harkokin kasuwanci,” in ji Musa. Ya sha alwashin cewa shi da iyalansa za su sadaukar da rayuwarsu a kan addinin Islama. A nasa jawabin, wani yayan Musa Abubakar, Alhaji Adamu Sabon Birni, ya ce “ta’addancin ’yan bindiga masu garkuwa da mutane ne ya yi ajalin mahaifina.
“’Yan bindiga ne suka kashe shi bayan karɓa kuɗin fansa har Naira miliyan 9 amma hakan bai sa na yi ridda ba, saboda matsalar ta’addancin ’yan bindiga ba iya Sakkwato kaɗai ake fama da ita ba.
“A duk faɗin Arewa ana fuskantar wannan matsala kuma mahukunta na iya ƙoƙarinsu wajen magance ta.
“Saboda haka a yanzu muna farin ciki ya gane kuskuren da ya yi kuma ya sake karɓar addinin Musulunci.
Matan Musa Abubakar da aka zanta da su sun ce za su iya ƙoƙari wajen goyon bayan mijinsu don ganin ya ci gaba da zama a Sakkwato kuma ya dawwama a kan tafarkin addinin Islama.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Sakkwato Jihar Taraba Musa Abubakar ya sake karɓar addinin Musa Abubakar ya yi ridda yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Abubuwan da suka sa Fafaroma Francis ya yi fice a duniya
Da safiyar wannan Litin fadar Vatican ta sanar cewa da misalin ƙarfe 7.35 Agogon Vatican Fafaroma Francis, wanda sunansa na asali Cardinal Jorge Mario Bergoglio, ya rasu a yayin da al’ummar Kirista na duniya ke bikin Ista.
Ya mutu ne washegari da ya fito bainar jama’a a Dandalin St Peter’s, domin taya Kiristoci murnar zagayowar ranar Ista.
Fafaroma Francis ya yi fama da doguwar jinya, inda a watan da ya gabata ne aka sallame daga asibiti bayan ya shafe makonni biyar can sakamakon cutar sanyin haƙarƙari mai tsanani.
Ga wasu abubuwa da Fafaroman ya yi fice a kansu:
1. Nuna adawa a fili ga wasu manufofin Donald Trump.Ya yi Allah wadai da yunƙurin Trump a mulkinsa na farko na gina katanga tsakanin Amurka da ƙasar Mexico, inda ya ce hakan ba ɗabi’ar Kiristoci ba ce.
Ya kuma yi Allah wadai da shirin maida baƙi ƙasashensu, da gwamnatin Trump ke ƙoƙarin yi a mulkinsa na biyu.
2. Sumbatar ƙafafuwan fursunoni.Fafaroma Francis ya wanke tafin ƙafafuwan wasu fursunonin gidan yarin Rome, tare da sunbata, abun da ya ja hankalin duniya.
3. Kira a magance matsalar sauyin yanayi.Fafaroma Francis ya zargi manyan ƙasashen duniya da ƙin ɗaukar matakan kare muhalli da sauyin yanayi, inda a 2023 ya ce wasu matsalolin ba za su taɓa gyaruwa ba.
4. Jawo masu ɗabi’ar auren jinsi a jiki.Duk da kakkausan suka da ya sha, wasu na ganin yana da ƙoƙarin jawo masu raunin imani a jiki, ciki kuwa har da yarda da ya yi ake sanya albarka ga auren jinsi.
5. Shi ne Fafaroma na 266, kuma na farko daga nahiyar Arewa da Kudancin Amurka.Asalin iyayensa ’yan Italiya ne, da suka yi ƙaura zuwa ƙasar Argentina. An haife shi a Buenos Aires, ranar 17 ga watan Disamba, 1936.
6. Kakkausar suka ga kamfanonin ƙera makamai.Ya yi kira ga ƙasashen duniya da su rungumi masalaha wajen magance rigingimu, gudun kada rikice-rikice su haifar da Yaƙin Duniya na 3.
7. Alaƙanta kwararar ’yan ci-rani zuwa Turai, da tauye ci-gaban ƙananan ƙasashe.Ziyararsa ta farko, Francis ya je tsibirin Lampedusa, yankin da ’yan ci-rani suke bi wajen shiga nahiyar Turai, inda ya ɗora laifi kan yadda ake tauye ci-gaban ƙananan ƙasashen duniya.
8. Yana son ƙwallon ƙafa da kuma waƙe-waƙe.Francis shi ne Fafaroma da yafi mu’amala da matasa, wajen sauraron su, da kuma ƙaunarsa da ƙwallon ƙafa.