Aminiya:
2025-04-23@19:41:09 GMT

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano

Published: 2nd, April 2025 GMT

An yi jana’izar marigayi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi, a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda dubban jama’a suka halarta.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, sun halarci jana’izar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi.

Basakkwacen da ya yi ridda ya sake karɓar addinin Musulunci Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa

An gudanar da sallar jana’izar ne a Fadar Sarkin Kano da ke Kofar Kudu, inda Farfesa Sani Zahradden ya jagoranci sallar.

Dubban jama’a ne suka halarci jansiza5 marigayin.

Har ila yau, Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya halarci jana’izar.

Marigayi Alhaji Abbas Sunusi, ya rasu ne a daren ranar Talata a gidansa da ke Kano bayan doguwar jinya.

Ya rasu yana da shekara 92 a duniya.

An birne shi a makabartar Gandun Albasa.

Domin nuna alhini game da rasuwar marigayin, Gwamnatin Jihar Kano da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, sun dakatar da bukukuwan Sallar da suka shirya gudanarwa a yau Laraba.

Marigayi Galadima ya riƙe mukami mafi girma a Masarautar Kano, kuma shi ne mahaifin Abdullahi Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano.

Ga hotunan yadda jana’izar ta gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barau Kwankwaso masarauta rasuwa Sarkin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai

Nahiyar dake da yawan mutane fiye da biliyan 1.4 na da babbar kasuwa. Matakin Donald Trump ka iya samar wa kasashen nahiyar damar karfafa hadin gwiwarsu da inganta tsarin masana’antu. Ban da wannan kuma, kasashen Afirka suna iya samun mafita ta hanyar kara hadin gwiwa da kasashe masu tasowa musamman ma kasar Sin.

 

Cikin shekaru 16 a jere ne Sin take kan matsayin abokiyar ciniki mafi girma ga Afirka. A maimakon matakin da Amurka ke dauka wato kara dora wa kasashen Afirka haraji, Sin tana dukufa kan taka rawar gani cikin tsarin hadin gwiwar mabambantan bangarori da gaggauta hadin gwiwar kasashe masu tasowa da cin moriya tare, matakin da zai samar da yanayi mai dorewa ga bunkasarsu baki daya.

 

Kazalika, ba kamar yadda Amurka ta kakkaba wa kasashen Afirka harajin da yawansa ya kai tsakanin 10% zuwa 50% ba, Sin ta soke dukkan harajin kwastam ne a kan kasashen da suka fi koma baya wadanda suka kulla dangantakar diflomasiyya tsakaninsu da Sin, ciki har da wasu kasashen Afirka 33, matakin da ya samar wa Afirka damammaki masu kyau wajen more manyan kasuwannin Sin.

 

Muna iya gani daga wadannan alkaluma cewa: Wane ne ya dunkula hannu kuma wane ne ya bude hannun runguma?, Wane ne ya kafa shingaye kuma wane ne ya gina gada? Girman kai da matukar son kai na zubar da mutumcin da kimar Amurka, yayin da kuma a maimakon haka, kuma matakin bude kofa da hadin gwiwa da Sin ke dauka na kara bayyana nagartaccen mutumci da martabar kasar. (MINA)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Iyalen Surajo Malumfashi na Radio Nigeria Kaduna Yana Gayyatar Jama’a Zuwa Daurin Auren ‘Yar Sa
  • Za A Yi Jana’izar Fafaroma Francis A Ranar Asabar A Vatican
  • HOTUNA: Pantami ya kai wa Sheikh Jingir ziyarar ta’aziyya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis
  • HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato
  • Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi