Aminiya:
2025-04-28@08:07:32 GMT

Mutum 2 sun rasu, 13 sun ɓace a hatsarin jirgin ruwa a Bayelsa

Published: 2nd, April 2025 GMT

Mutum biyu sun rasa rayukansu, yayin da ake ci gaba da neman wasu mutum 13 da suka ɓace yayin wani hatsarin jirgin ruwa a Jihar Bayelsa.

Hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Talata, lokacin da jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya yi karo da wani jirgin kamun kifi.

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Galadiman Kano Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus

Masu nutso a ruwa sun fara ƙoƙarin ceto waɗanda suka ɓace.

Bayanai sun nuna cewar wani jirgi mai suna ‘Meeting Marine’ wanda ya taso daga Anyama Ijaw zuwa Lubia da Foropa ya yi karo da jirgin kamun kifi.

Jirgin na da injin 115HP kuma wani mutum da ake kira Saturday ne yake tuƙa shi.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ruwa a Bayelsa, Kwamared Ogoniba Ipigansi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa har yanzu ba a samo mutum 13 ba.

Ya ƙara da cewa matsalar rashin ingantaccen yanayin sadarwa a yankin na hana aikin ceto tafiya yadda ya kamata.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Bayelsa, DSP Musa Muhammad, ya ce ba a kai musu rahoton faruwar lamarin ba tukuna, amma sun fara bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa Hatsarin Jirgin Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

Ƴan fashi sun sace fasinjoji guda bakwai a cikin motocin haya biyu a ƙauyen Eleyin da ke cikin ƙaramar hukumar Isin a Jihar Kwara.

A cewar rahoton LEADERSHIP, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:45 na yamma a ranar Juma’ar da ta gabata, lokacin da wasu ƴan fashi su biyar suka toshe hanya, suka tsayar da motoci biyu, sannan suka tilasta ɗaukar dukkanin fasinjojin zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, daga cikin fasinjojin motar ɗaya, akwai shugaban sashin shari’a na ƙaramar hukumar Oke Ero, Barr. Elizabeth Arinde, da daraktan gudanar da ma’aikata na wannan ƙaramar hukumar, Alh. Musbau Amuda.

Kakakin Ƴansanda na Jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an sami ceto fasinjoji biyu, Ganiyu Ajayi da Kolawole Adeyemi. Ta kuma ƙara da cewa, har yanzu ana ƙoƙarin ceto sauran fasinjojin guda biyar da kuma kama ƴan fashin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara
  • An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
  •  Adadin Wadanda Su ka Kwanta Dama A Gobarar Tashar Jirgin Ruwan Shahid Raja’i Sun Kai 21
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Jikkata Mutane Masu Yawa
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Lashe Rayukan Mutane A Kudancin Iran
  • Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo
  • An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
  • An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano