Tun daga ranar 1 ga watan Afrilu, dakarun rundunar sojojin ’yantar da al’umma ta kasar Sin ko PLA shiyyar gabashin kasar ta kaddamar da atisayen hadin gwiwar rukunoni masu kunshe da sojojin kasa, da na ruwa, da na sama da dai sauransu a kewayen tsibirin Taiwan. Atisayen da ya kasance wani salo na jan kunne mai karfi ga mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan”, kana mataki mai karfi da ya wajaba na kare ikon mulkin kai da cikakkun yankunan kasar Sin.

Kamar yadda aka sani, Taiwan wani sashe ne na kasar Sin, wanda ba ta taba zama kasa ba, kuma ba zai taba zama ba a nan gaba. Sunan yankin Taiwa a MDD shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar ba.

A daya hannun, matakin da babban yankin kasar Sin ya dauka ya nunawa kasashen duniya tsayayyiyar niyyar kasar ta tabbatar da nasarar warware batun Taiwan, da cimma manufar dinke dukkanin sassan kasar yadda ya kamata, kana ba za ta taba amincewa da duk wasu rukunoni ko mutanen dake neman balle Taiwan daga kasar Sin ba. Kowane karin girman kai da mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan” suka yi, za a bi shi da hukunci mai karfi daga babban yankin kasar Sin, kuma karshensu zai zo da wuri. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.”

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
  • Xi Jinping Ya Bukaci A Hada Karfi Wajen Farfado Da Kasar Sin
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare
  • Gwamna Buni Ba Zai Shiga Hadakar Jam’iyyun Adawa ba – Mai Magana Da Yawunsa