Tun daga ranar 1 ga watan Afrilu, dakarun rundunar sojojin ’yantar da al’umma ta kasar Sin ko PLA shiyyar gabashin kasar ta kaddamar da atisayen hadin gwiwar rukunoni masu kunshe da sojojin kasa, da na ruwa, da na sama da dai sauransu a kewayen tsibirin Taiwan. Atisayen da ya kasance wani salo na jan kunne mai karfi ga mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan”, kana mataki mai karfi da ya wajaba na kare ikon mulkin kai da cikakkun yankunan kasar Sin.

Kamar yadda aka sani, Taiwan wani sashe ne na kasar Sin, wanda ba ta taba zama kasa ba, kuma ba zai taba zama ba a nan gaba. Sunan yankin Taiwa a MDD shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar ba.

A daya hannun, matakin da babban yankin kasar Sin ya dauka ya nunawa kasashen duniya tsayayyiyar niyyar kasar ta tabbatar da nasarar warware batun Taiwan, da cimma manufar dinke dukkanin sassan kasar yadda ya kamata, kana ba za ta taba amincewa da duk wasu rukunoni ko mutanen dake neman balle Taiwan daga kasar Sin ba. Kowane karin girman kai da mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan” suka yi, za a bi shi da hukunci mai karfi daga babban yankin kasar Sin, kuma karshensu zai zo da wuri. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba

Kakakin rundunar tsaron teku ta kasar Sin Liu Dejun, ya bayyana a yau Lahadi cewa, an kori wani jirgin kamun kifi na kasar Japan da ya shiga yankin ruwan kasar Sin na tsibirin Diaoyu Dao ba bisa ka’ida ba.

A cewarsa, rundunar ta dauki matakan da suka dace bisa doka, ta gargadi jirgin sannan ta kore shi, bayan ya shiga yankin ruwan kasar Sin tsakanin ranar Asabar da Lahadi.

Sau Biyu Ake Yin Girbin Aya A Shekara – RMRDC Gwamnatin Yobe Ta Ƙaryata Rahoton Bayyanar Boko Haram A Babban Birnin Jihar

Da yake bayyana tsibirin na Diaoyu Dao da tsibiran dake karkashinsa a matsayin mallakin kasar Sin, Liu Dejun ya bukaci Japan ta gaggauta dakatar da ayyukanta da suka saba doka a wadannan yankuna.

Har ila yau, rundunar ta ce, za ta ci gaba da ayyukanta na tabbatar da doka a yankin ruwa na tsibirin Diaoyu Dao da kare yankuna da hakkoki da muradun kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
  • Sabon Tsarin Harajin Kwastam Na Amurka Ya Kwace ‘Yancin Sauran Kasashe
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • Mutane 2 Sun Yi Shahada A Wani Hari Da Jirgin Sama Maras Matuki Na HKI Ya Kai Wa Kasar Lebanon
  • Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya
  • An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito
  • Pezeshkian ya soki barazanar Amurka kan kasarsa game da tattaunawar nukiliya
  • Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba
  • Babban Mashawarcin Gwamnatin Wucin-Gadi Ta Kasar Bangladesh Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG