Gwamnatin Nijar, ta saki ministocin hambarariyar gwamnatin Bazoum
Published: 2nd, April 2025 GMT
Gwamnatin Nijar ta saki kusan mutane 50 da suka hada da ministocin da aka tsare tun bayan da sojoji suka hambarar da gwamnatin Mohamed Bazoum a watan Yulin 2023.
Baya ga tsaffin ministocin da akwai wasu sojoji da ake zarginsu da yunkurin juyin mulki a shekarar 2010 da suma aka sake su.
“An sako wadannan mutane ne bisa ga shawarwarin da babban taro na kasar ya bayar,” kamar yadda sakataren gwamnatin kasar ya karanta a gidan talabijin din kasar a cikin daren jiya.
Cikin tsaffin ministocin da aka saki har da tsohon ministan man fetur Mahamane Sani Issoufou, dan tsohon shugaban kasar Mahamadou Issoufou, da kuma tsohon ministan tsaro Kalla Moutari, da tsohon ministan kudi Ahmat Jidoud, da kuma tsohon ministan makamashi Ibrahim Yacoubou.
An kuma saki sojojin da a baya aka samu da laifin yunkurin juyin mulki da kuma janyo “barazana ga tsaron kasar”, ciki har da Janar Salou Souleymane, da tsohon babban hafsan hafsoshin sojin kasar, da wasu jami’ai uku da aka yankewa hukuncin daurin shekaru 15 a shekarar 2018 a gidan yari, saboda kokarin hambarar da Shugaba Issoufou a shekarar 2015.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
Wani magidanci ya ɗankara wa matarsa saki a ofishin ’yan sanda bayan an kama ta a wani otel.
Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa an kama matar ce a yayin wani samame da ’yan sanda suka kai maɓoyar dillalan miyagun ƙwaya da ’yan sara-suka a wasu otel-otel a garin Minna.
Ya bayyana cewa sai bayan da aka kawo matar ofishin ’yan sanda, a yayin bincike suka gano cewa matar aure ce, bayan da suka tuntuɓi ’yan uwan mutanen da aka kama.
Ya ce, “Sakamakon yawaitar yadda matasa suke tayar da zaune tsaye ne mataimakin gwamna Kwamred Yakubu Garba, ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki a kansu.
Yadda uba da ɗansa da wani ango suka rasu a bakin aiki a Bauchi Fafaroma Frasncis ya rasu yana da shekaru 88“Shi ne muka kai samame, muka kama mutanen da ake zargi, cikinsu har da mata. Abin mamaki sai ga wani mutum ya zo, cewa ɗaya daga cikin matan da muka kama mai ɗakinsa ce, kuma nan take ya yi mata saki uku.
“Ba mu san cewa matar aure ba ce, kuma ba mu da masaniyar abin da ya kai ta wurin, domin ’yan sanda ba su kammala bincike ba lokacin da mutumin ya je ya ba ta takarda a ofishin ’yan sanda.”