Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya nanata shirin Tehran na shiga tattaunawar da Amurka kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya, yana mai gargadin cewa barazanar soji daga Amurka na dagula halin da ake ciki a yanzu.

“Jamhuriyar Musulunci, kamar yadda ta kasance a baya, a shirye take don yin shawarwari na hakika,” in ji Araghchi a wata wayar tarho da takwaransa na Holland, Caspar Veldkamp, yau Laraba.

Ya jaddada cewa wannan “yana bukatar yanayi mai kyau da kuma nisantar hanyoyin da suka shafi barazana.”

Ministan ya yi Allah wadai da barazanar da jami’an Amurka suka yi wa Iran da cewa “ba za a amince da su ba”, ya kara da cewa sun saba wa kundin tsarin mulkin MDD da dokokin kasa da kasa, hasali ma suna “rikitar” halin da ake ciki.

Araghchi ya yi gargadin cewa Iran za ta mayar da martani “cikin gaggwa” ga duk wani cin zarafi a kan iyakokinta, huruminta, da kuma muradun kasarta.

A halin da ake ciki kuma, ya soki kungiyar Tarayyar Turai kan gazawarta na daukar matsaya kan kalaman na jami’an Amurka, wadanda ya ce suna barazana ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

A nasa bangaren, Veldkamp ya bayyana damuwarsa game da karuwar tashe-tashen hankula a yankin, yana mai jaddada bukatar hanyoyin diflomasiyya wajen warware takaddamar.

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar a karshen mako cewa zai iya ba da umarnin kai hare-haren soji kan Iran idan Tehran ta ki shiga tattaunawa don “saka sabuwar yarjejeniya” kan shirinta na nukiliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba

Kungiyar gwagwarmaya ta Ansarullah ta bayyana cewa yarjejeniyar tsagaiat wutar da ta cimma da Amurka, ba ta sauya matsayin kasar ba na kai wa Isra’ila hari.

Kakakin kungiyar Ansarullah Mohammed Abdul-Salam ya jaddada cewa Dakarun Yeman za su ci gaba da kai hare-hare kan Isra’ila domin goyan bayan Falasdinawa a zirin Gaza.

Yarjejeniyar da Amurka ba ta da alaka da matsayinmu na goyan bayan Gaza, inji Abdul-Salam.

A jiya ne masarautar Oman ta sanar cewa Amurka da kungiyar Ansarullah da aka fi sani da ta ‘yan Houtshis a Yeman suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Bayan tattaunawa da tuntubar juna da aka yi a baya-bayan nan da kuma tuntubar juna tsakanin masarautar Oman ta Amurka da hukumomin da abin ya shafa a birnin Sana’a na jamhuriyar Yeman, an samu cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu.

Sanarwar ta kara da cewa: A nan gaba, ko wanne bangare ba zai kai hari kan daya ba, ciki har da jiragen ruwan Amurka a tekun Bahar Rum da Bab al-Mandab, domin tabbatar da ‘yancin zirga-zirgar jiragen ruwa da kuma tafiyar da harkokin kasuwancin kasa da kasa cikin sauki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin
  • Sharhin bayan Labarai: Mahangar Iran Dangane Da Tattaunawa Kan Shirinta na Makamashin Nukliya Na Zaman lafiya
  • Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya
  • Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
  • Aragchi Ya Ce Hanyar Diblomasiyya Ce Kadai Hanar Warware Matsalar Shirin Nukliyar Iran
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
  • Hamas : Tattaunawar sulhu ba ta da wani tasiri a halin da ake ciki
  • Hannayen jarin kamfanonin fina-finan Amurka sun fadi sakamakon barazanar Trump na kakaba harajin kwastam
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
  • Kasar Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wani Hari Da Zata Fuskanta Daga Makiya