HausaTv:
2025-04-23@19:25:49 GMT

ICC ta yi kakkausar suka ga Hungary saboda yin watsi da sammacin kama Netanyahu

Published: 2nd, April 2025 GMT

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) mai hedkwata a birnin Hague ta yi Allah-wadai da matakin da kasar Hungary ta dauka na kin mutunta sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da zai ziyarci kasar da ke tsakiyar Turai a ranar Alhamis.

Mai magana da yawun kotun, Fadi El Abdallah, ya fada yayin wani taron manema labarai cewa, bai kamata mambobin kotun ICC su yi watsi da hukuncin kotun ba.

Kakakin ya ci gaba da cewa dole ne mambobin kotun su aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke.

Ana sa ran Netanyahu zai isa Budapest a yammacin yau Laraba don ziyarar kwanaki hudu, bisa gayyatar Firaministan Hungary Viktor Orbán.

Shugaban na Hangari mai tsatsauran ra’ayi ya gayyaci takwaransa na Isra’ila duk da tuhumar da ake yi wa Netanyahu a hukumance da laifin amfani da yunwa a matsayin hanyar yaki da kuma aikata laifukan cin zarafin bil’adama a Gaza.

Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC ta bayar da sammacin kama Netanyahu da tsohon ministansa na yaki, Yoav Gallant, bisa zargin laifukan yaki da cin zarafin bil adama a ranar 21 ga Nuwamba, 2024.

An bayar da sammacin ne bayan tantance akwai “kwararen dalilai ” dake cewa Netanyahu da Gallant “da gangan sun hana farar hula a Gaza abuban more rayuwa, ciki har da abinci, ruwa, da magunguna da kuma man fetur da wutar lantarki.” A Gaza.

A matsayinta na mamba a kotun hukunta manyan laifuka ta ICC, dole ne Hungary ta kama Netanyahu da zarar ya isa a tsakiyar nahiyar Turai tare da mika shi ga kotu, saidai duk da haka Hungary, ta fito karara cewa ba za ta mutunta hukunci da bukatun kotun ta ICC ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Netanyahu da

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi

Hukumar Hisbah ta kama wata mata mai sana’ar ɗan wake kan zargin ta da yin lalata da wani almajiri dan shekara 14 a garin Azare da ke Jihar Bauchi.

Shugaban Hukumar ta Hisbah na shiyyar Katagum da ke Azare, Malam Ridwan Muhammad  Khairan ya bayyana cewar, ana zargin matar, wadda ake kira Baba Mai Ɗan Wake da laifin yin fasikanci ta hanyar tilasawa da yaudara da wani almajiri dan kimanin shekaru 14, bayan ta sanya masa maganin ƙarfin maza a cikin lemon kwalba don ya riƙa biya mata buƙata.

Ya ce almajirin ya haɗu da Nana Mai Ɗan Wake da yake mata wanke-wanke a Sabuwar Tashar Jama’are ne, a cikin garin Azare, inda ta buƙaci ya riƙa zuwa gidanta yana kwana, inda ta rika yaudarar sa har ta riƙa yin lalata da shi.

A cewar Malam Ridwan Mohammed Khairan, sun cafke matar ne bayan samun labari cin zarafin almajirin ta hanyar neman sa da ya riƙa biya mata buƙata irin ta mata da miji. Ya ce almajirin da kansa ya gudu ya nemi mai unguwa domin a kuɓutar da shi daga wannan hali da ta sanya shi ciki.

Don haka suka kai rahoton ga Hukumar Tsaron Farin Kaya Sibli Difens (NSCDC) aka kamo ta aka yi mata binciken kwakwaf, daga nan aka kai ta Bauchi ofishin masu binciken manyan laifika (CID) don kammala binciken kafin a mika ta ga kotu.

Wata majiya ta ce wajen da matar take sana’ar dan waken ya zama babban dandalin ɓarayi da ’yan shaye-shaye da ƙananan mata masu zaman kansu, domin duk wadda aka kama a samame, takan ce a wajen baba mai ɗan wake take.

Da aka tambayi almajirin abin da ke faruwa tsakaninsa da ita? Ya ce da farko bara yake zuwa, sai ta ce, ya rika zuwa gidanta tana ba shi abinci.

Ya ce da yake zuwa gidanta bayan ta tashi a kasuwancinta, sai ta riƙa kai shi ɗakinta tana ba shi abinci da lemon kwalbar da take sa maganin a ciki, tare da umartar sa ya riƙa matsa mata jikinta daga nan sai ta rika jan sa kanta tana kama gabansa tana sawa a cikin nata.

Yaron ya ce haka suka rika yi tun kafin azumi har bayan azumi, alhali shi ba abin da yake ji sai ciwon baya da yake addabar sa, wanda hakan ta sa ya gudu ya yi ƙara wajen mai unguwa.

Yanzu dai Shugaban Ƙungiyar Alarammomi na Ƙasar Katagum, Alaramma Husaini Gwani Gambo da Ƙungiyar Mata Musulmi ta FOMWAN da Ƙungiyar Matasa Masu Neman Hakkin Dan Adam, sun sa hannu don ganin an yi hukunci a kanta da bukatar tashinta a garin Azare.

Shugaban ƙungiyar alarammomin ya tabbatar da cewar, za su yi duk yadda za su yi don ganin an bi musu hakkin wannan cin zarafin da aka yiwa almajirinsu ba don ganin ya zama darasi ga wasu irin ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Rohoton Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Ya Tabbatar Da Tafka Manyan Laifukan Cin Zarafin Bil-Adama A Siriya
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI