Aminiya:
2025-04-24@16:04:11 GMT

IMF ta nemi Tinubu ya kyautata rayuwar talakawan Najeriya 

Published: 3rd, April 2025 GMT

Asusun Bada Lamuni na Duniya (IMF), ya buƙaci Gwamnatin Najeriya da ta tabbatar da cewa manufofin tattalin arziƙin ƙasar sun kare muradun mutane masu rauni.

Daraktar Hulɗa da Jama’a na IMF, Julie Kozack, ta bayyana hakan a yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Washington, D.C.

NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansu Uromi: Barau ya ziyarci iyalan waɗanda aka kashe, ya ba su kyautar N16m

Ta jaddada muhimmancin bai wa talakawan Najeriya masu fama da ƙuncin rayuwa tallafin kuɗi sakamakon sauye-sauyen tattalin arziƙi.

Aminiya ta ruwaito cewa cire tallafin man fetur, wanda IMF ta ba da shawara a kai, ya haifar da tashin farashin man fetur daga kimanin Naira 200 kan kowace lita zuwa sama da Naira 1,000.

Wannan sauyi ya jefa ’yan Najeriya da dama cikin matsananciyar wahala.

Duk da haka, Kozack ta amince da ƙalubalen da jama’a ke fuskanta kuma ta jaddada buƙatar tallafa wa masu ƙaramin karfi.

Ta buƙaci gwamnati da ta mayar da hankali kan shirye-shiryen jin daɗin al’umma, kamar bayar da tallafin kuɗi, tare da inganta hanyoyin tara kuɗaɗen shiga na cikin gida.

Haka kuma, ta sanar da cewa jami’an IMF za su ziyarci Najeriya nan ba da daɗewa ba domin nazarin manufofin tattalin arziƙi na shekarar 2025 a ƙarƙashin shirin bincike na ‘Article IV’, wanda ke tantance yanayin tattalin arziƙin ƙasashe mambobin IMF.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Talakawa Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya

Babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya ba da umarnin ga rundunar sojin Najeriya da ta fatattaki ‘yan bindigar da ke addabar al’ummar kananan hukumomin Baruten da Kaiama na jihar kwara da Borgu da ke dajin Kainji a jihar Neja cikin wata guda.

 

A jawabin da ya yi wa dakarun rundunar soji bataliya ta 22  a Sobi Ilorin, Oluyede ya ce sojojin Najeriya ba za su bari tashin hankalin yankin arewa maso gabas ya rikide zuwa arewa ta tsakiya ba.

 

A cewarsa nauyi ne da ya rataya a wuyan sojojin Najeriya su kare martabar yankunan kasar.

 

Shugaban hafsan sojin ya ce dole ne a fatattaki ‘yan bindigar daga yankin Najeriya nan da wata guda.

 

Oluyede ya kara da cewa, rundunar soji ta samar da Uniform guda 100,000 yayin da aka ware naira miliyan dubu domin ciyar da sojojin a kowane wata.

 

A kwanakin baya ne wata kungiyar da aka fi sani da Mahmuda ta bulla a kananan hukumomin Kaiama da Baruten na jihar Kwara yayin da wasu da ba a tantance ba suka kashe mutane bakwai a Ilesha Baruba da ke karamar hukumar Baruten a jihar Kwara ranar Litinin.

COV/ALI RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci
  • IMF: Rashin Tabbas Zai Dagula Tattalin Arzikin Duniya
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Nda-Isaiah Ta Yaba Wa Matar Shugaban Kasa Tinubu Kan Soyayya Da Tallafawa Talakawan Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
  • Kiristoci Sun Yi Zanga-zanga, Sun Nemi Adalci Kan Kisan Gilla