Jami’ar Bayero Ta Kaddamar da shirin amfani da adaidaita Sahu wajen zirga zirga a Jami’arA wani gagarumin yunkuri na bunkasa zirga zirga da walwalar dalibai, Shugaban Jami’ar Bayero Kano Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya kaddamar da shirin amfani da babura masu kafa uku ko adaidaita a harabar jami’ar a hukumance.

Wannan yunƙurin na nufin samar wa ɗalibai da ma’aikata hanyar sufuri mafi aminci, mafi dacewa, da sauƙaƙe ƙalubalen da ke tattare da zirga zirga tsakanin sassan jami’ar.

Shugaban jami’ar wanda ya samu rakiyar magatakarda Haruna Aliyu da mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Haruna Musa da shugaban dakin karatu na jami’ar Dr. Kabiru Dahiru Abbas da shugaban hulda da jama’a na jami’ar Lamara Garba da Farfesa Yakubu Magaji Azare, Shugaban jami’ar ya jaddada kudirin hukumar ta BUK na ba da fifiko ga walwalar dalibai.

 

“Wannan shiri wani bangare ne na kokarin da muke yi na inganta tsaro da walwala ga dalibanmu.

 

Mun himmatu wajen sanya cibiyoyin karatunmu ba wai kawai su karfafa ilimi ba har ma da kwanciyar hankali da aminci ga kowa da kowa,” in ji Farfesa Abbas.

Ya kuma tabbatar wa da al’ummar jami’ar cewa za a yi amfani da kekunan ne ta hanyar sanya ido da kuma tantancewa, tare da horar da direbobin yadda ya dace su gudanar da aikin su a harabar jami’ar daga karfe 7 na safe zuwa 9 na dare.

Shugaban jami’ar ya kara da karfafawa dalibai cewa su yi amfani da wannan damar tare da kasashin za a kara yawan daidaita din domin biyan bukatun daliban da ma’aikata

Wannan ci gaban ya biyo bayan dokar hana babura da jami’ar ta yi a watan Fabrairun 2025 saboda matsalolin tsaro.

Gabatar da kekuna masu kafa uku ya fi aminci, kuma ingantaccen tsari ne da zai tabbatar da zirga zirga cikin harabar jami’ar cikin kwanciyar hankali.

 

Khadijah Aliyu Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Bayero Shugaban Jami ar Shugaban jami ar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jinjinawa kasashen Sin da Rasha a matsayin abokan hulda na kut-da-kut da kasar, yayin da ya isa birnin Beijing domin yin shawarwari da manyan jami’an kasar Sin, gabanin yin tattaunawa zagaye ta uku da Amurka kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Abbas Araghchi ya shaida wa kafar yada labaran Iran a babban birnin kasar Sin a ranar Laraba cewa, “Sin da Rasha abokan hulda ne na kut da kut da suka tsaya tare da mu a lokutan wahala, don yana da kyau da ma’ana mu ci gaba da tuntubar juna tare da su a bangarori daban-daban, musamman ma yanzu da ake tattaunawa da Amurka.”

“Ya zama dole mu sanar da abokanmu a kasar Sin cikakken bayani game da al’amuran da ke gudana tare da tuntubarsu.” Inji shi.

Yayin da yake jaddada cewa, ya yi irin wannan ganawa da manyan jami’an kasar Rasha a birnin Moscow a makon jiya, Araghchi ya ce yana fatan samun kyakkyawar tattaunawa da mahukuntan Beijing, domin isar da sakon shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ga mahukuntan kasar Sin.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce, “A baya kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa kuma mai ma’ana a batun nukiliyar kasar Iran, kuma ko shakka ana bukatar hakan.

Za mu ci gaba da tuntubar Sin a matsayinta na mamba a kwamitin sulhun MDD, mamba a kwamitin gudanarwar hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, bugu da kari kawa  ta kut-da-kut ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inji ministan harkokin wajen kasar ta Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure
  • Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci
  • Nda-Isaiah Ta Yaba Wa Matar Shugaban Kasa Tinubu Kan Soyayya Da Tallafawa Talakawan Nijeriya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Shugaban Ma’aikatar Shari’a Yana Halartar Taro A Kasar China
  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis