Aminiya:
2025-04-24@15:53:59 GMT

INEC ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha kiranye

Published: 3rd, April 2025 GMT

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana cewa buƙatar da wasu suka shigar don yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Mazaɓar Kogi ta Tsakiya kiranye, bai cika sharuɗa ba.

INEC ta ce yunƙurin bai cika sharuɗan Sashe na 69(a) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanadar ba.

Bello Turji ya kashe manoma 11 a wani sabon hari a Sakkwato  NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ‘Ya’yansu

Wannan sanarwa ta fito ne daga shafukan sada zumunta na INEC a ranar Alhamis, 3 ga watan Afrilu, 2025.

Wasu ƙungiyoyi sun yi ƙoƙarin yi wa Sanata Natasha kiranye, wanda suka ce Sanatan na neman jefa su cikin rikicin da ka iya hana su samun romon dimokuraɗiyya.

Ƙungiyoyin sun miƙa ƙorafinsu ga INEC bisa hujjar cewa ba ta yi musu wakilci mai kyau ba.

Sun yi iƙirarin tattara sama da sa hannun mutum 250,000 daga cikin masu kaƙa ƙuri’a kimanin 480,000 da ke yankin.

Sanata Natasha, ta fuskanci ƙalubale a siyasa a baya-bayan nan, ciki har da dakatarwar tsawon watanni shida d Majalisar Dattawa ta yi mata bisa zargin aikata rashin ɗa’a.

Ta ƙalubalanci wannan hukunci, inda ta bayyana cewa an dakatar da ita ne saboda zargin cin zarafi da ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

Wannan batu ya haddasa muhawara mai zafi kan haƙƙin mata da yanayin siyasar Najeriya.

Yadda INEC ta yi watsi da buƙatar tsige ta na nuni da tsauraran sharuɗan da ake buƙata kafin batun kiranye ya samu ƙarbuwa.

Wannan yana jaddada yadda ake buƙatar bin dokoki da tsari kafin a iya aiwatar da yi wa wani ɗan majalisa kiranye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kiranye Majalisar Dattawa

এছাড়াও পড়ুন:

Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya

Wata ƙungiyar masu iƙirarin jihadi da ake kira Mahmuda tana ci gaba da kafuwa da ƙara ƙarfi tare da addabar jama’a a wasu garuruwa na ƙananan hukumomin Ilesha Baruba da Kemaanji da Kaiama da Baruten na Jihar Kwara.

Bayanai sun ce ’yan ƙungiyar sun sami mafaka ne a gandun dajin Kainji Lake National Park, kuma daga can ne suke kai hare-hare a garuruwan da ke makwabtaka da dajin har ma da wasu sassa na Jihar Neja.

DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030

Bayanai sun ce ko a Juma’ar da gabata sai da mayaƙan suka kashe wasu fulani huɗu, ɗan sa-kai da wani saurayi mai shekaru 19.

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan ta’addan da suka yi shiga ta kakin soji haye a kan babura sun kai harin ne yayin da ake tsaka da cin wata kasuwar dare, inda suka buɗe wuta kan mai uwa da wabi sannan suka arce.

Rahotanni na cewa sabuwar ƙungiyar tana kashe-kashe da garkuwa da mutane a ƙauyukan Kemaanji, Tenebo, Baabete, Nuku, da Nanu a ƙananan hukumomin Kaiama da kuma yankunan Yashikira na Ƙaramar Hukumar Baruten gami da yankunan Babana da Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja.

‘Za mu tabbatar da tsaro a yankin Gandun Daji na Kainji’

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq yayin wata ziyara da kai wuraren da abin ya shafa tare da manyan jami’an tsaro, ya ce ’yan ta’addan na kai wa ’yan sa-kai harin ne a matsayin ramuwar gayya saboda matsin lambar da suke yi musu.

Da kuma yake jawabi a fadar Sarkin Kaiama, Alhaji Muazu Shehu Omar, gwamnan ya ce za su yi duk mai yiwuwa tare da sojoji da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin Gandun Daji na Kainji.

Yanzu haka dai mutanen garuruwan da abin ya shafa suna ta yin hijira zuwa wasu wurare, domin guje wa ƙwazzabar ’yan ƙungiyar ta Mahmuda.

Mazauna yankin sun ce dama can ’yan ƙungiyar ta Mahmuda ta taɓa kafa sansani a ƙananan hukumomin Kaiama da Baruten, inda suka nuna cewa babu ruwansu da mutanen gari kuma hakan ya sa mutanen suka saki jiki da su.

Mazauna sun ce da farko Mahmudawan sun soma yaɗa da’awa ta Musulunci, amma daga baya suka fara ɗaukar wasu matasa a matsayin mayaƙa da masu tattaro musu bayanai.

Wani mazaunin yankin ya ce daga baya ne Mahmudawan suka fara yawo da makamai suna kama mutanen gari da kuma yanke musu hukunci har ma da kashe wasu. “Sun fi shekara 5 da fara bayyana”

Ya ƙara da cewa a wannan karon da suka dawo ”Daga gabas da gari zuwa yamma, mutum baya da halin zuwa gona mai nisan kilomita biyu haka.

“Gaba ɗaya na tsorata, kashi 50 cikin ɗari na mutanen gari sun gudu.”

Haka nan kuma ƙungiyar ta Mahmuda ta haramta wa mutanen Kaiama da Baruten noma “kashi 95 cikin 100 na mutanenmu manoma ne.

“To yanzu sun ce ba mu da damar yin noman ka ga dai yanzu mutuwa ta fuskance mu, ba ma yunwa ba.”

“Mun sha ankarar da mahukunta kan ayyukan ’yan ƙungiyar amma ba a ɗauki mataki ba, amma sai a kwanan ne sojoji suka yi musu ruwan wuta a maboyarsu, in ji wani mazauni, Haruna Idirissa.

Wasu rahotanni na cewa ’yan ƙungiyar wani tsagi ne na ƙungiyar Boko Haram da Abubakar Shekau ya jagoranta, da suka fito daga wani sashe na ƙasashen Benin da Nijar, sai dai suna da sassaucin tsaurin ra’ayi.

Mun tanadi tsaro — ’Yan sanda

Tuni dai Kakakin rundunar ’yan sandan Kwara, Adetoun Ejire-Adeyemi a wata sanarwa da ya fitar, ya musanta ɓullar ƙungiyar, yana mai cewa ko labarin da ake yaɗawa na cewa sun kashe ’yan sa-kai 15 ba gaskiya ba ne.

Sai dai rundunar ta bai wa mazauna tabbacin tanadar tsaro ingantacce domin wanzar da zaman lafiya.

Rundunar ta kuma buƙaci mazauna da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar kiyaye duk wata doka, tana mai kiran da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da wata fargaba ba.

Muna zaune cikin fargaba —Basarake

Sarkin Yashikira, Alhaji Umaru Seriki, ya bayyana cewa a yanzu haka suna zaune cikin fargaba saboda ta’adar sabuwar ƙungiyar da ke musu barazana a kodayaushe.

Tun a shekarar 2022 Majalisar Dattawa ta bayyana fargaba

A shekarar 2022 ce Majalisar Dattawa ta yi iƙirarin cewa sabuwar ƙungiyar ta samu mafaka a wasu ƙananan hukumomi uku na jihohin Kwara da Neja.

Majalisar Dattawan a wancan lokacin ta yi kira da babbar murya, inda ta nemi hukumomin tsaro da su ɗauki ƙwararan matakai kan ’yan bindigar da duk wani ɓurɓurshi na miyagu da ke addabar yankin Gandun Daji na Kainji.

Aminiya ta ruwaito cewa, Sanatan Kwara ta Tsakiya, Sadiq Umar tare da Mataimakin Bulaliyar Majalisar, Sanata Aliyu Abdullahi mai wakiltar Neja ta Arewa ne suka gabatar da wannan ƙudiri.

A watan jiya ne ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya, Zagazola Makama, ya ba da rahoton cewa ’yan sa-kai sun kama wani ɗan bindiga da ya bayar da bayanan sirri kan ayyukan ƙungiyar.

A halin yanzu dai bayan ɓullar Mahmudawa, ƙungiyoyin ta’adda masu tayar da ƙayar baya na ci gaba da ƙaruwa a ƙasar.

Ƙungiyoyin ta’addan da ake fama da su a Nijeriya sun haɗa da Boko Haram, ISWAP, Lakurawa, Ansaru da kuma ta bayan nan Mahmuda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  • Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa
  • Sahel: CILSS ta yi gargadi game da sake bullar ‘’kwarin dango’’ a yankin sahel
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi