Hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta bayyana cewa takardar neman tsige Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta tsakiya a Majalisar Dattawa, ba ta cika sharuɗɗan doka da kundin tsarin mulki ya tanada ba.

INEC ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa takaitacciya da ta wallafa a shafinta na Facebook yau Alhamis, tana cewa: “Takardar neman tsige Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya ba ta cika sharuɗɗan da ke cikin sashi na 69(a) na kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ba.

INEC Ta Karɓi Takardun Yi Wa Sanata Natasha Akpoti Kiranye  Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha

Sai dai hukumar ta yi alƙawarin fitar da cikakken bayani kan wannan ci gaba nan ba da jimawa ba.

Rahoton wakilinmu ya nuna cewa har yanzu ba a tabbatar ko masu ƙorafin za su samu damar gyara takardar domin dace wa da doka ko kuma za a yi watsi da ita gaba ɗaya ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata

A daidai lokacin da  sake bude yaki a Gaza ya cika kwanaki 57,sojojin HKI suna ci gaba da kai hare-hare akan al’ummar Gaza da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa da dama.

Cibiyar watsa labaru ta Falasdinu ta sanar da cewa; Sojojin na HKI sun kai hare-hare masu yawa a sassa mabanbanta na gaza wanda ya fara tun daga watan Maris, da hakan ya kara jefa Falasdinawa cikin wahala, bayan yunwar da suke fama da ita.

Da safiyar yau Talata sojojin na HKI sun kai hare-hare  sau 3 a garin Abasan a gabashin Khan-Yunus.

A cikin birnin Gaza kuwa sojojin na HKI sun baje wasu gidaje da kasa a karo na uku.

A garin Khan-Yunsu wani matashi mai suna Amid Hamdun al-Qudrah, ya yi shahada.

A unguwar “Shuja’iyyah” ma wani Bafalasdine mai suna Muhammad Mu’in  al-Ja’abari ya yi shahada sanadiyyar raunin da ya samu a harin baya.

A unguwar “Zaytun” kuwa sojojin na HKI su kai hare-hare ne har sau 8 a yau Talata.

A daren jiya wasu Falasdinawa 3 daga iyali 1 sun yi shahada a cikin tantin ‘yan hijira a yankin ‘al’amudi’ a arewacin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Gaza
  • Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
  • Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Buƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Gudanar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Jabaliya Da Khan Yunus
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC
  • Kashi 42 Na Ma’aikatan Jinya Na Niyyar Barin Afirka Saboda Rashin Albashi – WHO
  •  Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
  • 2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido