Madatsar Tiga Za Ta Samar Da Ruwan Sha A Garin Rano
Published: 3rd, April 2025 GMT
A kokarin magance matsalar karancin ruwan sha da garin Rano ke fuskanta na tsawon shekaru, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da ta fara amfani da Madatsar Tiga don samar da ruwa mai a garin.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Dr.
Gwamna Yusuf ya yaba wa Sarkin Rano bisa jajircewarsa wajen kare muradun al’ummarsa, inda ya tabbatar masa da cewa gwamnati na daukar matakan da suka dace domin shawo kan matsalar ruwa a garin.
Ya bayyana cewa an riga an tsara shirin gina rijiyoyin burtsatse tare da hadin gwiwar ƙaramar hukumar, duk da cewa duwatsu da ke karkashin kasa na kawowa aikin cikas.
A kwanan nan ne gwamnatin jihar Kano ta gudanar da bincike domin tabbatar da lafiyar Madatsar ta Tiga, wacce za ta rika samar da ruwa a garin na Rano.
Haka kuma, madatsar tana dauke da tashar samar da wutar lantarki mai nauyin megawatt 10, wacce aka kammala gina ta a shekarar 2023.
Gwamna Yusuf ya nanata kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta bangarori da dama, ciki har da noma, kiwon lafiya, muhalli, ilimi, da kuma karfafawa mata da matasa.
A nasa bangaren, Sarkin Rano, Ambasada Dr. Muhammad Isa Umar, ya gode wa Gwamna Yusuf bisa ci gaban da ake samu a masarautar, tare da rokon sa da ya ci gaba da mayar da hankali kan matsalar samar da ruwa.
Sarkin ya kuma yaba wa gwamnan bisa daukar mataki kan koke-koke da aka gabatar game da aikin titi mai nisan kilomita biyar, wanda hakan ya kai ga nusanya dan kwangilar da ya kasa yin aikin da wani wanda ya fi kwarewa.
Ziyarar gaisuwar Sallah ta kasance mai kayatarwa, inda aka gudanar da wasanni na gargajiya, ciki har da shahararrun mawakan garaya na Masarautar Rano, waɗanda suka nishadantar da jama’a.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Rano Ruwan Sha samar da ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana farin cikisa bisa da shirye-shiryen da Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa NAHCON, ta gudanar ya zuwa yanzu, domin aikin Hajjin shekarar 2025.
Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ne ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin tattaunawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa, bayan da ya jagoranci membobin hukumar ta NAHCON domin gabatar wa Mataimakin Shugaban Ƙasa bayanai kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2025.
Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa ne ke sa ido kan ayyukan NAHCON, kuma Hukumar ta shaida wa Sanata Kashim Shettima cewa an kammala dukkan shirye-shiryen da suka wajaba domin fara aikin Hajjin 2025 da jigilar mahajjata zuwa ƙasar Saudiyya daga ranar 9 ga Mayu, 2025.
A nasa jawabin bayan ganawar, Kwamishinan NAHCON mai kula da ayyuka, Prince Anofi Elegushi ya bayyana cewa an riga an kammala shirye-shirye a Makka, Madina da sauran wurare domin gudanar da aikin Hajji cikin sauki.
Ya ce, “Mun tanadi masaukai a Makka, da Madina da sauran wurare, an kuma shirya su domin tarɓar mahajjatanmu, inda muka samu isassun gadajen, tare da biyan kuɗin abinci mai kyau kuma isasshe ga dukkan mahajjata. Mun zaɓi ranar 9 ga watan Mayu domin tashin jirgin farko zuwa Madina, muna kuma fatan kammala jigilar zuwa Saudiyya kafin ranar 24 ga watan Mayu, kuma mu fara dawo da mahajjata daga ranar 13 ga Yuni har zuwa 2 ga Yuli.”
A jawabinsa tun da farko, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya bukaci Hukumar da ta tabbatar da cewa kowa yana bakin kokarinsa domin tabbatar da nasarar aikin Hajjin bana.
“Ya zama wajibi a dauki dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da nasarar aikin Hajjin 2025. Wannan nauyi ne a kanmu ga ‘yan Najeriya da mahajjata, domin mu tabbatar da aikin Hajji mai inganci.” In ji shi
Safiyah Abdulkadir