Aljeriya ta bukaci taron gaggawa a kwamitin tsaro kan Falasdinu
Published: 3rd, April 2025 GMT
Aljeriya ta kira taron gaggawa na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya domin tattauna halin da Falasdinu ke ciki.
Bayan karuwar laifuffukan da yahudawan sahyoniyawa da suke aikatawa a kisan gillar da suke yiwa Palastinawa a yankin zirin Gaza da kuma ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahyoniya suka yi a yammacin gabar kogin Jordan, Aljeriya ta bukaci gudanar da wani taron gaggawa na kwamitin sulhu kan halin da Falasdinu ke ciki.
Kasar Aljeriya ta ba da misali da karuwar hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan Falasdinawa da ta mamaye musamman a yankin zirin Gaza a matsayin dalilin bukatar gudanar da wannan zama. Sama da wata guda kenan da Gaza ke cikin wani mummunan yanayi, ana kashe jama’a ciki har da ma’aikatan agaji.
An kuma gabatar da wannan bukata bayan gano gawarwakin ma’aikatan agaji 15 da ma’aikatan jin kai da daukin gaggawa a Gaza wadanda ke da alaka da kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu, da kungiyar kare fararen hula ta Falasdinu, da kuma Majalisar Dinkin Duniya.
An kuma bayyana karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan sahayoniya mazauna Yammacin Kogin Jordan ke haifarwa a matsayin wani dalili na neman wannan taron gaggawa.
A zamansa na 58, Kwamitin Kare Hakkokin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da wani kuduri kan halin da ake ciki na kare hakkin bil’adama a yankunan Falasdinawa da suka mamaye ciki har da gabashin birnin Kudus .
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, an amince da kudurin ne a ranar Laraba inda kasashe 27 suka amince, 4 suka nuna adawa, sannan kasashe 16 suka kaurace kada kuri’ar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: taron gaggawa Aljeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
Da yake jawabi a fadar Mai Tangele (Sarkin Billiri), Danladi Sanusi Maiyamba, ya bayyana lamarin da matukar bakin ciki tare da fatan samun makoma mai kyau ga wadanda suka rasu, ya kuma warkar da wadanda suka samu raunuka da gaggawa.
Daga nan sai Gwamna Inuwa ya sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan 2 kowanne ga iyalai biyar da suka rasa rayukan ‘yan uwansu, wanda ya kai adadin zuwa Naira miliyan 10.
Ya kuma yi alkawarin biyan kudaden jinya ga wadanda ke karbar magani a Asibitocin jihar.
A yayin da yake godiya, Sarki Maiyamba ya ce, hatsarin na Easter ya girgiza daukacin masarautar Tangale, amma ya amince da matakin da gwamnatin jihar ta dauka, wanda ya ce hakan ya taimaka wajen hana barkewar rikici a yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp