Dakarun Yemen Sun kai hari kan jirgin ruwan yaki na Amurka USS Harry Truman da makamai masu linzami
Published: 3rd, April 2025 GMT
Dakarun Yaman sun sanar da mayar da martani kan harin baya-bayan nan da Amurka ta kai kan kasarsu, wanda ya hada da hare-hare ta sama har sau 36 a yankuna da dama a cikin gundumomin Sanaa, Sa’ada, da wasu jahohin kasar, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar mutane da dama.
Kakakin Rundunar sojin Yaman Birgediya Janar Yahya Saree ya tabbatar da cewa, sojojin Yaman sun gudanar da wani shiri na soji na hadin gwiwa, inda suka yi arangama da jirgin ruwan Amurka Harry Truman da jiragen yakin da yake dauke da su a arewacin tekun Bahar Maliya.
Saree ya ci gaba da cewa, a harin an yi amfani da makamai masu linzami da kuma jirage marasa matuka, kuma harin ya cimma nasara kamar yadda aka tsara, inda ya ce an dauki tsawon sa’o’i da dama ana gudanar da farmakin, kamar yadda kuma a lokaci guda sojojin Yeman sun dakile wani bangare na harin Amurka.
Ya kuma kara tabbatar da cewa dakarun na Yemen za su ci gaba da kai hare-hare kan dukkanin jiragen ruwan yakin Amurka da kuma jiragen da suka keta dokar hana shiga yankunan da aka ayyana, yana mai bayyana cewa wadannan hare-haren wuce gona da iri na Amurka ba za su hana su cika alkawarin da suka dauka na tallafawa al’ummar Palasdinu ba.
Saree ya tabbatar da cewa sojojin Yeman na ci gaba da gudanar da ayyukansu a cikin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, kuma ba za su gushe ba har sai an dakatar da kai farmaki a kan Gaza tare da kawo karshen killacewar da ake yi wa al’ummar yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
Gwamna Umar Mohammed Bago, ya sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 12 a birnin Minna na Jihar Neja.
Wannan dai na zuwa ne sakamakon hare-haren da ya janyo salwantar rayuka da aka samu a bayan nan a babban birnin.
Hanyoyin da za a magance rikicin Filato — Masana HOTUNA: Yadda Pantami ya kai wa Sheikh Jingir ziyarar ta’aziyyaA cewar gwamnan, an haramta zirga-zirgar baburan ’yan acaɓa da masu Keke Napep daga ƙarfe 6 na yamma zuwa 6 na safiyar kowacce rana.
Gwamnan ya bayyana hakan a yayin wani taro na musamman da ya gudana da masu ruwa da tsaki kan sha’anin tsaro da ya ƙunshi sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a Fadar Gwamnatin jihar a ranar Talata.
A yayin da dokar ba ta shafi duk wata buƙatar lafiya ta gaggawa, Bago ya ce ba a buƙatar ganin ababen hawa daga lokacin da dokar ta fara aiki da zummar daƙile matsalar tsaro da babban birnin ke fuskanta.
Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta zuba ido a yayin da miyagu ke ci gaba da kai hare-hare da kashe mutanen da ba su ji ba kuma ba su gani ba.
Ya umarci dukkan dagatai da masu unguwanni da su tabbatar da ɗaukar bayanan duk wasu baƙi da suka shigo yankunansu.
Kazalika, ya yi gargaɗin cewa duk gidan da aka kama yana bai wa miyagu mafaka ko masu fataucin muggan ƙwayoyi za a rushe shi.
A ’yan kwanakin nan dai birnin Minna na fuskantar matsalar tsaro da ta haɗa da dabanci, hare-hare da kisan kai da sauran miyagun ababe masu ɗaga hankalin mazauna.