Burundi ta zargin Rwanda da yunkurin kai mata hari
Published: 3rd, April 2025 GMT
Shugaban kasar Burundi ya yi gargadin cewa Rwanda na da shirin kai wa kasarsa hari, bayan da sojojin Burundi suka taimakawa Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango (DRC) a yakin da take yi da ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda.
Shugaban kasar ta Burundi Evariste Ndayishimiye ya bayyana cewa, ya samu “sahihan bayanan sirri” da ke nuni da shirin Rwanda na kai wa Burundi hari, ko da yake bai bayar da karin bayani kan shirin da yake yin zargin a kansaba, wanda Rwanda ta musanta.
“Mun san cewa yana da shirin kai hari Burundi,” in ji Ndayishimiye a wata hira da wata kafar yada labarai yayin da yake magana kan shugaban kasar Rwanda Paul Kagame, yana mai jaddada cewa “‘yan Burundi ba za su amince a kashe su ba kamar yadda ake kashe ‘yan Kwango, mutanen Burundi mayaka ne.”
Ministan Harkokin Wajen Rwanda, Olivier Nduhungirehe, ya kira wadannan kalamai na shugaban Burundi da cewa “abin takaici ne” ya kuma kara da cewa a cikin wani sakon da ya wallafa a shafin X cewa kasashen biyu sun shiga tattaunawa, bayan da suka amince kan wajibcin kawar da duk wani mataki na soja.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin DRC da ‘yan tawayen M23, yayin da ‘yan tawayen da ke samun goyon bayan Rwanda ke ci gaba da kwace filayensu duk da cewa kasashen biyu na kokarin tsagaita wuta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Dabbobi 4 A Wani Hari A Filato
Ya roƙi matasa da su zauna lafiya kuma su riƙa kai rahoton duk wani abu na barazana ga jami’an tsaro, domin nemo mafita game da hare-haren da ke ci gaba da faruwa.
Garba Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da makiyayan shida ke kiwo.
“Da maharan suka fara harbi, ɗaya daga cikin makiyayan da ya tsira ne ya kira ya ba mu labari. Ina samun labarin, na garzaya wani shingen sojoji da ke Latiya, inda na kai rahoto. Daga nan jami’an tsaro tare da ni muka tafi wajen, mun tarar da shanun da tumakin da aka kashe,” in ji shi.
Shugabannin ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da GAFDAN a jihar, Ibrahim Babayo da Garba Abdullahi, sun yi kira ga hukumomin tsaro da su binciki lamarin tare da hukunta waɗanda suka aikata laifin.
Haka kuma sun roƙi mambobinsu da su zauna lafiya kuma ka da su ɗauki doka a hannunsu, su bar hukumomin tsaro su ɗauki mataki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp